• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2022 Taron Makon Likitoci: Kebbi Ta Yi Asarar Kwararrun Likitoci 10 Cikin Shekara Guda – NMA

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
2022 Taron Makon Likitoci: Kebbi Ta Yi Asarar Kwararrun Likitoci 10 Cikin Shekara Guda – NMA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar likitocin Nijeriya (NMA), reshen Jihar Kebbi, ta koka da cewa a kasa da shekara guda akalla likitoci 10 ne suka bar jihar zuwa kasashen waje.

Shugaban kungiyar, Dokta Murtala Muhammad-Dandare ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin
  • Ruhin Hanyar Ruwa Ta Red Flag Zai Ci Gaba Da Kasancewa Har Abada

Shugaban ya yi jawabi ne a yayin kammala taron kimiyya mai taken makon Likitoci na shekara 2022 watau ( Physicians’ Week) wanda kungiyar NMA reshen Jihar Kebbi ta shirya a Birnin Kebbi.

Dokta Muhammad-Dandare dai ya koka da cewa: “Yadda likitoci da sauran ma’aikatan lafiya ke barin kasar nan a kullum abin tsoro ne, a nan jihar Kebbi cikin kasa da shekara guda sama da kwararru goma ne suka bar Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (FMC) da ke Birnin Kebbi.

“Kwararren Likita (Consultant) shi ne wanda ke horar da kananan likitoci, wannan babbar barazana ce ba ga jihar Kebbi kadai ba har ma da kasar Nijeriya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Saboda ya kamata gwamnati da saurari masu ruwa da tsaki don hada kai, don yin abin da ya dace da kuma magance wannan matsala.”

Kazalika, ya tuna cewa a makon da ya gabata ne shugabansu na kasa, Dokta Roland Ogema ya sanar da cewa, kimanin likitoci 900 ne suka bar Nijeriya zuwa kasashen ketare cikin kasa da wata guda, inda ya tabbatar da cewa lamarin na da matukar tayar da hankali, inji Dokta Murtala Muhammad-Dandare Shugaban kungiyar NMA ta kasa reshen Jihar kebbi”.

A cewarsa, likitocin da suka yanke shawarar ci gaba da zama a Nijeriya suna da yawa, suna masu korafin cewa WHO ta kayyade rabon abinci na likita guda ga mutane 600, amma a Nijeriya, likita daya ya kai mutane 6,191, wanda ba ya wadatar sosai.

Shugaban ya ce manufar taron shi ne a hada kwararru a fannin kiwon lafiya domin tattaunawa kan batutuwan da suka shafi kiwon lafiya da yadda za a inganta su.

Shi ma a wata hira, babban mai gabatar da jawabi, Farfesa Nasiru Muhammad, farfesa a fannin ilimin ido daga Jami’ar Usman Danfodio (UDUSOK), da ke Jihar Sakkwato , ya ce taron wanda shi ne taron shekara-shekara, ya mayar da hankali ne kan tsarin kiwon lafiyar Nijeriya “a wannan mawuyacin lokaci da tarihin mulkin demokradiyya a kasar.”

Wakilinmu ya ruwaito cewa” an gabatar da wata takarda mai taken: “Tsarin Bayar da kiwon Lafiyar Nijeriya da Tsarin Dimokuradiyya na 2023 Lokaci ne don Canja yanayi”.

Shehin malamin, wanda kuma shi ne babban mai ba da shawara ga likitan ido kuma (sabbatical consultant),a Babbar Asibitin gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, watau FMC ya lura cewa Nijeriya na da manyan abubuwan da za su iya amfani da su, amma ba za su iya yin amfani da irin wannan damar ba.

Har ilayau, ya koka da cewa idan har akidar ci gaban bil’adama a Nijeriya za ta kai 0.36 ma’ana wanda aka haifa a kasar nan zai iya samun karfin ikonsa da kashi 36 cikin 100 kawai, inda ya kara da cewa adadin ba ya wakiltar koyarwar manyan addinan kasar nan.

Bugu da kari Likitan ido ya yi nuni da cewa ma’aikatun kiwon lafiya da ke da alhakin kula da harkokin kiwon lafiya sun fi mai da hankali kan wuraren da jama’a ke zuwa kamar Asibitoci masu zaman kansu ba a kula da su ba, sai dai mallakar gwamnati wanda basu da kayan aiki da kuma isasun ma’aikata.

“Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a shekara ta 2000 ta gudanar da wani bincike a duniya don duba tsarin kiwon lafiya da yadda suke gudanar da ayyukansu, don haka, daya daga cikin muhimman abubuwan da aka gano shi ne cewa ma’aikatun lafiya na kasashen duniya sun fi mayar da hankali kan abubuwan da ke faruwa a cikin jama’a.

“Ya kamata su ma su tsara kamfanoni masu zaman kansu, sun ba su izinin budewa, don ganin mutane sannan kuma su kai ziyarar gani da ido zuwa wuraren masu zaman kansu don duba abin da suke yi. Amma binciken ya nuna cewa an fi mayar da hankali ga Asibitoci jama’a mallakin gwamnati bisa ga ba da dama ga Asibitoci masu zaman kansu.

“A yawancin kasashe suna zuwa Asibitoci masu zaman kansu fiye da na gwamnati, ma’ana yawancin kiwon lafiyar da ake bayarwa ba ma’aikatun kiwon lafiya ne ke kula da su ba, wadanda ya kamata su kasance masu ruwa da tsaki a harkokin kiwon lafiyar kasar, amma ba su bane” in ji shi.

Don haka Farfesa Nasiru ya yi kira ga ma’aikatun lafiya na jihohi da na tarayya da su ci gaba da gudanar da ayyukansu da nufin ceto rayukan ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasashen WajeKebbiLikitoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

Next Post

An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

1 hour ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

3 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

6 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

7 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

7 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

8 hours ago
Next Post
An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata

An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.