• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Ibo mazauna Jihar Kano sun bayyana goyon bayan su ga ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, a babban zaɓen da za a yi a wannan watan.

 

Sarkin Ibo na Kano, wato Eze Ikechukwu Akpudo, shi ne ya bayyana haka a madadin al’ummar tasa a lokacin da sarkin yaƙin rundunar zaɓen Atiku a Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali-Amin (Little), ya kai masa ziyara a fadar sa.

  • Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

Eze ɗin ya bayyana Atiku da cewa wani kadarko ne wanda ya yi aiki matuƙa wajen kawo haɗin kai a ƙasar nan.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Ya ce: “’Yan Nijeriya ba su da zaɓin da ya wuce Atiku, domin shi kaɗai ne wanda zai iya doke Tinubu a zaɓe. Ya na takara a babbar jam’iyya.

 

“Wani dalilin kuma shi ne ba za mu iya goyon bayan tsarin takarar Muslim-Muslim ba. Mu na so a samu takara mai daidaito domin tabbatar da adalci ga kowa da kowa.

 

“Kamar yadda ku ke gani, kwanaki kaɗan ne su ka rage kafin a yi zaɓe, amma babu wani daga cikin mu da zai tashi ya koma garin su domin yin zaɓen. A nan za mu yi zaɓen tare da iyalan mu. Nan za mu tsaya, a nan mu ke harkokin kasuwancin mu.

 

“Addu’ar mu ita ce a yi zaɓe cikin lumana. Mun yanke shawarar cewa Atiku Abubakar kaɗai ne zai iya tunkarar matsalolin da ƙasar nan ke fuskanta a yau.

 

“Mu na magana ne da murya ɗaya a matsayin mu na al’umma ɗaya. Ba mu yin wata ƙunbiya-ƙunbiya a magana, kuma mu na ba mai girma Atiku tabbacin cewa shi za mu ba ƙuri’un mu.

 

“Ni ɗin nan sau biyu ana zaɓa ta a matsayin kansila a Sabon Gari. Zan tattaro jama’a bakin iyawa ta don ganin Atiku ya samu nasarar lashe zaɓen da za a yi.”

 

A nasa ɓangaren, Ali-Amin Little ya bayyana cewa ‘yan ƙabilar Ibo mutane ne masu son zaman lafiya kuma sun yi fice a harkar kasuwanci.

 

Ya yi kira a gare su da su yi amfani da ƙuri’ar su yadda ya kamata domin su samu cin moriyar mulkin dimokiraɗiyya tare da sauran al’umma.

 

Ya ce: “Atiku Abubakar zai yi tafiya tare da dukkan ƙabilu idan ya zama shugaban ƙasa. Ƙasar nan ta yi masa komai na rufin asiri, don haka shi ma ya ke so ya mayar mata da sakayyar alheri ta hanyar samar da shugabanci mai nagarta da alfanu ga ‘yan Nijeriya.

 

“Hakan ne ya sa ya ke auren mace Ibo, da Bayarabiya da Kanuri, da sauran su. Shi Waziri mutum ne da ya kamata ‘yan Nijeriya su amince da shi saboda amfanuwar ƙasar da haɗin kan ta.”

 

Wasu waɗanda su ka take wa Al-Amin Little sawu a lokacin ziyarar sun haɗa da Dakta Auwalu Anwar, wanda shi ne mai ba Atiku shawara a ɓangaren tsare-tsare, da kuma Alhaji Bashir Kalla.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

Next Post

Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

5 days ago
Next Post
Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.