• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mace 1 Ce Ta Fito Takarar Shugaban Kasa Da Wasu 380 A Kujerun Majalisar Tarayya – INEC

by Sulaiman
3 years ago

A jadawalin sunayen ‘yan takarar da ta fitar, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa an samu mace ɗaya tilo ta fito takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Hakan na ƙunshe cikin jerin sunayen da hukumar ta fitar a ranar Talata, mai ɗauke sa hannun Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye.

  • INEC Ta Dakile Yunkurin Kutse Cikin Rumbun Adana Bayananta – Farfesa Yakubu

Ya ce an samu mata har 380 da za a fafata neman kujerun Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa da su.

A jerin sunayen an lissafa mata 92 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu mata 288 da za a fafata neman kujerar Majalisar Tarayya da su.

A ɓangaren maza kuwa, INEC ta buga sunayen 1,008 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu 2,832 da za su fafata neman kujerun Majalisar Tarayya.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

INEC ta ce jam’iyyu 18 ne su ka shiga takarar zaɓen shugaban ƙasa, wanda za a fafata a ranar 25 ga Fabrairu, 2023.

“An samu masu takarar shugaban ƙasa da masu takarar mataimakin shugaban ƙasa har su 35 daga jam’iyyu 18. Akwai ‘yan takarar Majalisar Dattawa su 1,101, waɗanda a cikin su 92 mata ne. Sai kuma masu takarar Majalisar Tarayya su 3122.

“Za a yi takarar kujeru 109 a Majalisar Dattawa, sai kuma kujeru 360 a Majalisar Tarayya. Baki ɗaya kujeru 469 kenan.” Inji Okoye, wanda ya ƙara da cewa waɗannan ‘yan takara na majalisu sun zama 4,224 kenan.

Cikin waɗanda INEC ta wanke domin shiga takarar zaɓen Shugaban Ƙasa, har da Bola Tinubu na APC, Rabiu Kwankwaso na NNPP, Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.

Sai dai kuma duk da jam’iyyar ADC ta dakatar da Kachikwu ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, sunan sa ya fito a cikin waɗanda za su fafata.

A jerin sunayen masu takarar Majalisar Dattawa dai babu sunan Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na APC da Machina wanda su ke tankiyar cancantar shiga takarar a tsakanin su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Koka Kan Yawaitar Zubar Da Shara A Tituna A Jihar

Gwamnatin Kano Ta Koka Kan Yawaitar Zubar Da Shara A Tituna A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.