• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Wajibi Ne Kafafen Yaɗa Labarai Su Yi Wa Jam’iyyu Adalci A Lokacin Yaķin Neman Zabe

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: Wajibi Ne Kafafen Yaɗa Labarai Su Yi Wa Jam’iyyu Adalci A Lokacin Yaķin Neman Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

2023: Wajibi ne kafafen yaɗa labarai su yi adalci ga jam’iyyu a lokacin yaķin neman zabe.

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta fayyace wa kafafen yaɗa labarai dokoki da ƙa’idojin bai wa jam’iyyun siyasa lokuta daidai da juna a yayin kamfen.

  • Kada Wata Jam’iyya Ta Kuskura Ta Karɓi Tallafin Kuɗi Daga Ƙasashen Waje – INEC

Shugaban hukumar ne, Farfesa Mahmood Yakubu ya yi masu wannan bayani dalla-dalla, lokacin da ya ke jawabi wajen taron ƙara wa kakafen yaɗa labarai na talbijin da radiyo ilmin sanin makamar yayata jam’iyyun siyasa a yayin kamfen.

An shirya taron ne a cikin makon nan a Abuja, domin ƙara ɗora su kan hanyoyin da doka ta tanadar wajen tabbatar da bin ƙa’ida yayin yaƙin neman zaɓen 2023.

A ranar 28 ga Satumba ce INEC ta amince aka fara kamfen, kamar yadda Sashe na 94 (1) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

“Yayin da za a fara yaƙin neman zaɓen 2023, ya na da muhimmanci dukkan jam’iyyu, ‘yan takara, magoya bayan su da kafafen yaɗa labarai su sani cewa, su na da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da an gudanar da komai bisa yadda doka ta gindaya.

“Kada a riƙa yayata kalaman ƙiyayya, zage-zage, sakin-baki, kalaman tunzira jama’a ko harzuƙa wani ɗan takara, aibatawa ko muzantawa, cin zarafi, lahanta wani ko lalata kayan kamfen ɗin wata jam’iyya,” inji Yakubu.

“Sashe na 95 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya fayyace komai dangane da ƙa’idojin da ba a yarda a karya ba.

“Mun sha samun ƙorafe-ƙorafen hana jam’iyyun adawa samun damar yin amfani da kayayyaki mallakar gwamnati, kamar kafafen yaɗa labarai ko filayen yin kamfen.

“Ina jaddada cewa yin amfani da ƙarfin mulki a hana jam’iyyar adawa dama daidai da jam’iyya mai mulki a kafafen yaɗa labarai na gwamnati, haramun ne a dokar INEC Sashe na 95 (2,3,4,5,6).

“Kafafen yaɗa labarai na gwamnati kada su hana wata jam’iyya damar yayata manufofin ta daidai da lokacin da su ka bai wa jam’iyya mai mulki.”

Yakubu ya ce akwai hukunci da Dokar INEC ta tanadar ga kafar yaɗa labaran, wanda ya haɗa da cin tara ta naira miliyan biyu. “Amma idan aka sake karya dokar, to sai an biya naira miliyan biyar. Shi kuma shugaban kafar yaɗa labarai ko ma’aikatan da su ka karya dokar, za a ci su tara ta naira miliyan ɗaya, ko ɗaurin watanni shida a kurkuku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Murnar ‘Yancin Kai: ‘Yan Nijeriya Sun Gudanar Da Fareti A Birnin New York, Amurka

Next Post

Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

6 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

7 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

8 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

9 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

11 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

12 hours ago
Next Post
Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.