• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Wajibi Ne Kafafen Yaɗa Labarai Su Yi Wa Jam’iyyu Adalci A Lokacin Yaķin Neman Zabe

by Sulaiman
3 years ago
Neman Zabe

2023: Wajibi ne kafafen yaɗa labarai su yi adalci ga jam’iyyu a lokacin yaķin neman zabe.

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta fayyace wa kafafen yaɗa labarai dokoki da ƙa’idojin bai wa jam’iyyun siyasa lokuta daidai da juna a yayin kamfen.

  • Kada Wata Jam’iyya Ta Kuskura Ta Karɓi Tallafin Kuɗi Daga Ƙasashen Waje – INEC

Shugaban hukumar ne, Farfesa Mahmood Yakubu ya yi masu wannan bayani dalla-dalla, lokacin da ya ke jawabi wajen taron ƙara wa kakafen yaɗa labarai na talbijin da radiyo ilmin sanin makamar yayata jam’iyyun siyasa a yayin kamfen.

An shirya taron ne a cikin makon nan a Abuja, domin ƙara ɗora su kan hanyoyin da doka ta tanadar wajen tabbatar da bin ƙa’ida yayin yaƙin neman zaɓen 2023.

A ranar 28 ga Satumba ce INEC ta amince aka fara kamfen, kamar yadda Sashe na 94 (1) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

“Yayin da za a fara yaƙin neman zaɓen 2023, ya na da muhimmanci dukkan jam’iyyu, ‘yan takara, magoya bayan su da kafafen yaɗa labarai su sani cewa, su na da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da an gudanar da komai bisa yadda doka ta gindaya.

“Kada a riƙa yayata kalaman ƙiyayya, zage-zage, sakin-baki, kalaman tunzira jama’a ko harzuƙa wani ɗan takara, aibatawa ko muzantawa, cin zarafi, lahanta wani ko lalata kayan kamfen ɗin wata jam’iyya,” inji Yakubu.

“Sashe na 95 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya fayyace komai dangane da ƙa’idojin da ba a yarda a karya ba.

“Mun sha samun ƙorafe-ƙorafen hana jam’iyyun adawa samun damar yin amfani da kayayyaki mallakar gwamnati, kamar kafafen yaɗa labarai ko filayen yin kamfen.

“Ina jaddada cewa yin amfani da ƙarfin mulki a hana jam’iyyar adawa dama daidai da jam’iyya mai mulki a kafafen yaɗa labarai na gwamnati, haramun ne a dokar INEC Sashe na 95 (2,3,4,5,6).

“Kafafen yaɗa labarai na gwamnati kada su hana wata jam’iyya damar yayata manufofin ta daidai da lokacin da su ka bai wa jam’iyya mai mulki.”

Yakubu ya ce akwai hukunci da Dokar INEC ta tanadar ga kafar yaɗa labaran, wanda ya haɗa da cin tara ta naira miliyan biyu. “Amma idan aka sake karya dokar, to sai an biya naira miliyan biyar. Shi kuma shugaban kafar yaɗa labarai ko ma’aikatan da su ka karya dokar, za a ci su tara ta naira miliyan ɗaya, ko ɗaurin watanni shida a kurkuku.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Next Post
Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.