• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Za A Bai Wa ‘Yan Hijira Damar Kaɗa Kuri’a A Sansanoninsu – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: Ba Da Jimawa Ba Za Mu Wallafa Cikakken Sunayen Wadanda Aka Yi Wa Rajistar Katin Zabe – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke yi don ganin ta yi shirin gudanar da zaɓen 2023 da wuri, Shugaban IINEC Farfsa Mahmood Yakubu ya jaddada cewa aƙalla fiye da ‘yan gudun hijira milyan uku ne za su yi zaɓe a sansanoni daban-daban a ƙasar nan.

Yakubu ya ƙara da cewa tuni hukumar sa ta fara aikin tsame sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

  • 2023: Ba Da Jimawa Ba Za Mu Wallafa Cikakken Sunayen Wadanda Aka Yi Wa Rajistar Katin Zabe – INEC

Shugaban na INEC ya bayyana fara aikin tsame sunayen waɗanda su ka yi rajistar Mallakar katin zaɓe sau biyu ko fiye da haka cikin wannan makon a Abuja.

Ya bayyana haka lokacin da ya ke jawabi a wurin taron masu ruwa da tsaki, kan bitar fayyace ƙa’idojin zaɓe a sansanin masu gudun hijira, wanda aka shirya ranar Talata, a Abuja.

An shirya taron ne ranar Talata a Abuja, inda Yakubu ya ce sake nazarin tsare-tsaren ya zama wajibi, domin rabon da a sake bibiyar sa tun na ƙarshe da aka yi a 2018, kafin zaɓen 2019.

Labarai Masu Nasaba

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Ya ce ana nan ana kuma ci gaba da tsame sunayen da aka yi rajista sau biyu ko fiye da haka ana zubarwa, domin a tabbatar da cikakkun adadin yawan waɗanda za su mallaki katin rajistar zaɓe guda ɗaya tilo, kamar yadda doka ta tanadar.

Ya ce sai an kammala tsame sunayen masu rajistar fiye da sau ɗaya sannan za a bayyana ranar da za a liƙa sunayen masu rajista, kowa ya gani a faɗin ƙasar nan.

“A tsarin ganin an gudanar da zaɓuka cikin sansanin ‘yan gudun hijira, mu na so mu tabbatar cewa wannan tsari kamar yadda doka ta tanadar, ba a bar kowa a baya ba.

“Za mu tabbatar kamar yadda dokar zaɓe ta shimfiɗa cewa an gudanar da zaɓe a sansanin masu gudun hijira, kuma naƙasassu sun samu damar yin zaɓe da kuma waɗanda wani Ibtila’i na barin gidajen su ya shafe su, kamar ambaliya.”

Yakubu ya ce aƙalla akwai mutane miliyan uku a sansanonin gudun hijira daban-daban a ƙasar nan.

Ya ce taron sake nazarin su ya zama wajibi a yanzu, saboda masu gudun hijira ɗin sun ƙaru, sakamakon wasu dalilai, kamar ambaliya.

Ya ce a yanzu kuma za a bayar da himma wajen ganin an wayar da kan mazauna sansanonin gudun hijira dangane da muhimmancin zaɓe da kuma ƙa’idojin da doka ta shimfiɗa wajen gudanar da zaɓe a cikin masu gudun hijira.

Shugaban INEC ya musanta zargin da Gamayyar Ƙungiyoyin Kare Haƙƙin Jama’a (CSO) su ka yi wa INEC cewa ta karya dokar Sashe na 19(1) na Dokar Zaɓe, sashen da ya fayyace yadda INEC za ta liƙa sunayen waɗanda su ka yi rajista, domin kowa ya gani a ƙasar nan.

“Ba mu karya wata doka ba. Saboda har yanzu ana kan tantancewa da tsame sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da biyu tukunna. Idan lokacin da za mu liƙa sunayen ya yi, za mu sanar kowa ya sani, kuma ya gani.” Inji Yakubu.

Ya ce za a liƙa sunayen a dukkan mazaɓu 8,809 da ake da su a ƙasar nan a dukkan ƙananan hukimomi 774 a Nijeriya, kamar yadda Sashe na 19(1) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

Ya ce za a haɗa sunayen da aka yi rajista a baya-bayan nan tare da adadin miliyan 84 da ake da su a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-dumi: Shugaban Kwamitin Amintattu Na PDP Yayi Murabus

Next Post

Hajjin 2022: Gwamnatin Zamfara Ta Mayar Wa Alhazai 1,318 Naira 50,000 Kowanne

Related

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

2 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

4 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

5 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

6 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

7 hours ago
Next Post
Hajjin 2022: Gwamnatin Zamfara Ta Mayar Wa Alhazai 1,318 Naira 50,000 Kowanne

Hajjin 2022: Gwamnatin Zamfara Ta Mayar Wa Alhazai 1,318 Naira 50,000 Kowanne

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.