• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majiyoyi sun bayyana cewa wasu daga cikin gwamnonin jami’yyar PDP na shan matsinlamba don su sauya sheka zuwa APC. Majiyoyin sun tabbatar da cewa fadar shugaban kasa da jam’iyyar APC suna kara matsinlamba ga wasu gwamnonin PDP domin sauya sheka.

Kazalika, majiyoyin sun shaida cewa wasu daga cikin gwamnonin adawa suna cikin rudani sakamakon rikicin da ke cikin PDP, wanda da yawa daga cikinsu ke fargabar zai raunana damar samun sabon zangon mulkinsu na biyu.

  • Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
  • Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Matsinlambar na tilasta musu sauya sheka yana zuwa ne a yayin da PDP ke ci gaba da fuskantar rikice-rikice da suka haifar da rabuwar kawuna a jam’iyyar a halin yanzu.

Haka kuma majiyoyin sun bayyana cewa gwamnonin PDP suna cikin damuwa game da halin da aka kafa a Jihar Filato, inda kotuna suka tsige ‘yan majalisar jiha na PDP da wasu ‘yan majalisun tarayya saboda rikice-rikicen cikin gida da ba a warware ba a matakin kasa. Abun tsoron shi ne, idan rikicin ya ci gaba da tafiya a haka, kowanne dan takara da PDP ta zaba, ciki har da dan takarar gwamnonin da ke neman tazarce, kotu na iya kwace zaben cikin Ruwan sanyi.

Rahotannin sun bayyana cewa duk da shaharar gwamnan Umo Eno na Jihar Akwa Ibom, yana fuskantar wani kalubale daga wanda ya gada, Udom Emmanuel, wanda ke rike da karfin ikon tsarin siyasar PDP a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

Wasu sahihin rahotannin daga cikin gwamnatin sun shaida cewa Gwamna Eno ba zai iya sauya sheka zuwa APC ba tare da amincewar Emmanuel ba, domin yin hakan na iya jawo masa asarar goyon bayan mambobin majalisun kasa da na jihar, ciki har da sauran muhimman masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

An kuma tattaro cewa wani bangare na shirin fadar shugaban kasa shi ne, dukkan jihohin Kudu Maso Gabas su kasance na APC. Gwamnonin kamar Hope Uzodimma su ne kan gaban wajen yin matsinlamba ga Gwamnan Peter Mbah na Jihar Inugu, Aled Oti na Jihar Abiya da Chukwuma Soludo na Jihar Anambra don su sauya sheka zuwa APC. Duk da haka, rahotanni sun bayyana cewa Gwamnan Inugu bai bayar da cikakken amsa kan lamarin ba, Soludo ba ya son shiga APC saboda yana ganin zai iya samun nasara a jam’iyyarsa ta APGA.

A Jihar Jihar Zamfara kuwa, an gano cewa fadar shugaban kasa ta nuna sha’awarta na shigo da gwamnan cikin jam’iyyar APC. Duk da haka, daya daga cikin matsalolin shi ne, akwai wadanda ba sa son lamarin ya tabbata kamar karamin ministan tsaro, Bello Matawlale.

A cikin wata tattaunawa da aka yi da shi a ‘yan kwanakin nan kan shirin komawa APC, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce a halin yanzu yana nan a cikin PDP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Next Post

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

Related

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

1 hour ago
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Labarai

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

2 hours ago
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

3 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

6 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

14 hours ago
Next Post
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam'iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.