• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

by Sani Anwar
2 months ago
in Siyasa
0
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙungiyar Jihohin Arewa, Gwamnan Jihar Gwambe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa; Shugaba Bola Tinubu, ya cika alƙawuran da ya ɗauka a 2023, sannan kuma har yanzu yana kan ci gaba da cika su.

Gwamna Yahaya, ya bayyana haka ne a taron tattaunawa na kwana biyu da aka gudanar, kan haɗin gwiwar gwamnati da jama’a, wanda Gidauniya Ahmadu Bello (SABMF), ta shirya a Arewa House da ke Kaduna.  

ɗa yake jawabi a kan taken taron, “Tantance Alƙawarukan Zaɓe: ƙarfafa Haɗin Gwiwar Gwamnati da Jama’a ɗon Haɗin Kan ƙasa”, Gwamna Yahaya ya ce; yana magana ne a kana bin da ke sa demokuraɗiyya ta kasance mai ma’ana.

“Sakamakon wannan haɗuwa da muka yi da wakilan gwamnatin tarayya, wajibi ne mu farad a yin adalci da kuma abin da ya dace. Haɗin gwiwar Arewa da Gwamnatin Shugaba Tinubu, ya yi matuƙar haifar da sakamako mai kyau, kama daga samun ayyukan more rayuwa zuwa batun samar da tsaro.

  • Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

“A 2027, dole ne a rama wa kura aniyarta, ta hanyar bai wa Shugaba Tinuba cikakken haɗin kai wajen ci gaba da mulki a faɗin wannan ƙasa,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Gwamnan Jihar ta Gwambe, ya tunatar da cewa; a lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya tsaya a gabanmu a matsayin ɗan takara a yaƙin zaɓen 2023, ya yi wa Arewacin Nijeriya alƙawura na musamman. Kazalika, Arewa ta amince da manufofin shugaban ƙasar, ta kuma yi tsayin daka wajen zaɓensa, inda suka bayar da gudunmawa na kimanin kashi 60 cikin 100 na ƙuri’un da Tinubun ya samu.

“A yau, ga shi mun taru, domin yin nazari a kan waɗancan alƙawuran tare kuma da tantance irin ci gaban da aka samu ya zuwa yanzu, abubuwan da muka samu su ne; sauye-sauyen da aka samu duk kuwa da irin ƙalubalen da ake fuskanta a wannan ƙasa. Wannan na nuna cewa, demokuraɗiyyarmu za ta iya yin aiki ne kaɗai idan ana cika alƙawuran da aka ɗauka, sannan shugabanni ba za su iya aiwatar da alƙawuran ba har sai sun samu haɗin kan ƴan ƙasa.  

“Zan iya bugun ƙirji wajen bayyana irin ci gaban da yankinmu na Arewa ya samu. ɗon haka, muna yi wa shugaban ƙasa godiya dangane da waɗannan sabbin tsare-tsaren ci gaba da ya kawo mana, mafi yawan ayyukan day a gada daga gwamnatin da ta gabata, yanzu haka yana kan hanyar kammala su.” 

Ya bayyana ire-iren waɗannan ayyuka da suka haɗa da aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano, layin jirgin ƙasa na Kano zuwa Katsina zuwa Maraɗi, gyaran matatar mai ta Kaduna, aikin bututun iskar gas na Abuja, Kaduna, Kano da kuma ci gaba da aikin haƙar mai a Kolmani.

“Waɗannan ayyuka, ko shakka babu; za su kawo ci gaba a ɓangaren masana’antu da samar da tsaro a yankunanmu na Arewa,” in ji shi. 

Gwamna Yahaya ya ƙara da cewa, akwai kuma wasu sabbin ayyukan more rayuwar da ken an tafe, waɗanda suka haɗa da hanyoyi daban-daban a tsakanin jihohi kamar babbar hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, wadda za ta haɗa ƴan kasuwar Arewa da na Kudu da kuma shirin samar da harkokin nomad a zai shafi Arewa.

Bugu da ƙari, ya lissafo wasu da suka haɗa da faɗaɗawa tare da inganta cibiyoyin harkokin kiwon lafiya, wanda y ace; dukkanninsu suna nuni ga manufar da aka tsara, don inganta rayuwar al’ummar wannan yanki na Arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCArewaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

Next Post

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

Related

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

1 week ago
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

1 week ago
Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC
Siyasa

Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC

1 week ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Siyasa

Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu

2 weeks ago
Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
Labarai

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

2 weeks ago
Next Post
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.