• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 days ago
in Daga Birnin Sin
0
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayar da umarnin tattara ra’ayoyin jama’a masu amfani da kafar intanet yayin da ake tsara shirin raya kasa na shekaru 5-5 karo na 15, tsakanin 2025-2030.

Shirin raya kasa na shekaru 5-5 da Sin take yi, wani aiki ne na hangen nesa da zama cikin shiri da tsara tafarkin da za ta bi na cimma bunkasar tattalin arziki da kyautatuwar zamantakewar al’umma cikin shekaru 5-5.

Shin me umarnin tattara ra’ayoyin jama’ar intanet yake nunawa?

Na kan yi dariya idan na ji wasu na cewa akwai matsalolin take hakkin jama’a a kasar Sin, domin hakan na nuna cewa, ba su da masaniya kan ainihin yanayin da Sin take ciki ko kuma suna take gaskiya domin cikar wasu burikansu na boye. Kamar yadda hukumomin Sin kan bayyana a kullum, demokuradiyyar kasar ita ce, mai da hankali kan jama’a ta kowacce fuska, kuma ita ce demokuradiyyar da jama’a suke amfana da ita.

Wasu za su ce, to ta yaya za a tattara ra’ayoyin wadanda ba sa amfani da intanet? 

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Sadarwar intanet da lantarki da ruwa da sauran abubuwan bukatun jama’a na yau da kullum sun game baki dayan kasar Sin. Ni ganau ce ba jiyau ba, domin na yi tafiye-tafiye da dama, na shiga kauyukan kasar Sin, kuma cikinsu babu inda na ziyarta da ban ga wadannan abubuwa da na ambata ba.

Idan muka ajiye batun sadarwar intanet a gefe, majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ita ce majalisar koli mai tsara dokoki a kasar, kuma wakilanta na fitowa ne daga dukkan bangarori da yankunan kasar. Sabanin yadda muka saba gani a kasashenmu inda wakilan jama’a ke tarewa a babban birnin, wakilan jama’a a kasar Sin na komawa ne cikin al’ummominsu, kuma a nan suke tattaro ra’ayoyi da shawarwari da bukatun jama’a.

Yayin da ake bin tsarin demokuradiyya, to ya zama wajibi walwala da kwanciyar hankalin jama’a su zama a kan gaba. Ina da yakinin yadda gwamnatin Sin ke sauraron ra’ayin jama’a da aiki tukuru wajen kyautata rayuwarsu na da nasaba da yadda jama’ar ke da kishin kasa da kokarin tallafawa ayyukan gwamnati. Tsarin demokuradiyyar kasar Sin ya nuna yadda gwamnati ke sauke nauyinta na hidimtawa jama’a da yadda jama’ar suke sauke nauyinsu na ba da gudunmawa ga ci gaban kasa da kishin kasa da kiyaye dokoki.

Hakika irin wannan tsari shi ake kira da ainihin demokuradiyya kuma irinsa ne ya dace da galibin kasashen duniya musamman masu tasowa dake kallon kasar Sin a matsayin a bar koyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Next Post

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Related

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

16 hours ago
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

17 hours ago
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

18 hours ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

19 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

20 hours ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

21 hours ago
Next Post
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

LABARAI MASU NASABA

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.