• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Xi Jinping

Da misalin karfe 9 na safiyar yau Laraba 3 ga Satumba ne aka gudanar da gagarumin bikin tunawa da cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da Sinawa suka yi da mamayar dakarun Japan, da kuma yakin duniya na kin tafarkin murdiya a filin Tian’anmen na birnin Beijing bisa jigon “Tunawa da tarihi, girmama jarumai, martaba zaman lafiya da kuma samar da ci gaba”, inda aka yi gagarumin bikin faretin sojoji, tare da al’ummomin duniya don tunawa da wannan rana mai girma.

Cikin sautin wakar soja mai karfi, Xi Jinping dake tsaye cikin wata mota ya bi faffadan titin Chang’an ya duba faretin rundunonin sojoji, da na kayayyakin soja dake jere.

Yayin wannan biki, akwai rundunoni 45 (da jirage) da aka duba, kuma da farko an duba faretin rundunonin sojoji 13 dake fareti da kafa. Sojojin al’ummar Sinawa sun cimma sabon tsari bayan da aka yi musu kwaskwarima, inda a karon farko aka gabatar da nau’o’in sojoji 4, wato sojin kasa, da sama, da ruwa da roka, da rundunonin sojoji 4, wato sojojin sararin sama, da na yanar gizo, da na tallafin bayanai, da kuma sojoji masu ba da hidima. Ban da wannan kuma, dukkan rundunonin soja da yan sandan tsaron cikin gida, sun rike tutocinsu a wannan biki.

Bisa goron gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi musu, shugabanni 26 na kasashe da na gwamnatocin ketare sun halarci bikin. Sannan wasu shugabannin majalisun dokokin kasashe, da mataimakan firaministocin wasu kasashe, da manyan wakilai, da shugabannin hukumomin kasa da kasa, da tsoffin shugabannin siyasa na kasashe da dama su ma sun halarci bikin.

Ban da wannan kuma, an gayyaci jakadun ofisoshin jakadanci na kasashen waje dake kasar Sin, da jami’an ofishin jakadanci dake kula da harkokin soji, da wakilan kungiyoyin kasa da kasa dake zaune a kasar Sin, da abokai 50 da iyalansu daga kasashe 14 da suka hada da Rasha, da Amurka, da Birtaniya, da Faransa, da kuma Kanada.

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Shekaru 80 da suka gabata, al’ummar kasar Sin sun samu gagarumar nasara a yakin kin hare-haren sojojin Japan bayan shekaru 14 masu cike da wahalhalu, tare da bayyana cikakkiyar nasarar yaki da mulkin danniya a duniya. Sin ta fara yakin kin hare-haren ne tun daga farko har karshe a tsawon lokaci, kuma bisa gagarumar sadaukarwar al’ummun Sin, kasar ta bayar da goyon baya a babban fagen yaki na yaki da mulkin danniya a gabashin duniya, tare da ba da muhimmiyar gudummawa ga samun nasarar yaki da mulkin danniya a duniya. (Amina Xu, Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.