• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

by Sulaiman
2 days ago
in Labarai
0
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai yi jawabi a wani taro na habaka kasuwanci karo na biyar wanda AFSNET ke shiryawa.

 

Taron zai gudana daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Satumba na shekarar 2025, a Cibiyar Habaka Kasuwanci (SAFEX) ta ƙasar Algeria.

  • Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima
  • Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa an gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi taron na AfSNET karo na biyar a ranar 6 ga watan Satumba na 2025.

 

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa, taron zai gudana ne a gefen bikin baje kolin kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka karo na huɗu (IATF2025).

 

“Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Aljeriya za ta ɗauki nauyin gudanar da bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) sannan kuma bankin Afreximbank tare da haɗin gwiwar Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) da Sakatariyar Yankin Kasuwancin Nahiyar Afirka (AfCFTA) za ta shirya shi.

 

“Bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) zai samar da wani tsari na musamman kuma mai ƙima ga ‘yan kasuwa don samun kasuwa guda ɗaya ta Afirka ga sama da mutane biliyan 1.4 tare da habaka tattalin arzikin cikin gida na sama da dalar Amurka tiriliyan 3.5 da aka samar a ƙarƙashin yankin ciniki cikin ‘yanci na Nahiyar Afrika.

 

Taken taron na bana shi ne; ‘Ƙarfin Cikin Gida, Tasirin Duniya: Ƙarfafa gwamnatocin ƙasashen Afirka masu cikakken iko don samun ci gaba mai ɗorewa, yana nuna haɗin gwiwarmu don ba da damar gudanar da mulki na cikin gida don samun sakamako mai kyau na nahiyar.

 

“Sakamakon nasarar taron AfSNET karo na huɗu da aka gudanar a Kisumu na ƙasar Kenya, wanda ya tara gwamnoni sama da 45, magadan gari, shugabannin ƙananan hukumomi, masu zuba jari, da kuma abokan ci gaba daga ko’ina a nahiyar Afirka, taron na AfSNET ya jaddada muhimman dabaru na ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa wajen inganta kasuwanci cikin ‘yanci na nahiyar Afrika (AfCFTA).

 

“Taron ya gabatar da manyan tattaunawa, zaman zurfafa zuba jari, da hada-hadar B2B da B2G, wanda ya baiwa ‘yan ƙasashe damar gabatar da shirye-shiryen ci gaba da kuma gano hanyoyin samar da kuɗaɗe.

 

“Tare da mai da hankali sosai kan ci gaba da haɗin gwiwar yanki, taron na Kisumu ya kasance wani muhimmin dandali na tattara albarkatu da ƙarfafa haɗin gwiwa, da tsara hanyoyin da za a iya aiwatarwa da ajandar kasuwanci da ci gaban Afirka daga tushe.”

 

“An gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi akan muhimmin abu cikin tattaunawar da za’ayi lura da ƙwarewar sa akan tattalin arziƙi da shugabanci.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Next Post

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Related

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

44 minutes ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

3 hours ago
Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

5 hours ago
Next Post
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

September 5, 2025
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

September 5, 2025
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

September 5, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

September 5, 2025
Noma

An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila

September 5, 2025
Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.