• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

by Rabi'u Ali Indabawa
9 hours ago
in Tsaro
0
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mutum mai suna Eze Elechi Amadi ya bayyana dalilin da ya sa ya kashe ƙaninsa mai shekara 18, Otu Ifeanyi, a unguwar Kajola da ke Ƙaramar Hukumar Odigbo, Jihar Ondo.

Amadi, wanda ƴan sanda suka cafke tare da wasu mutum 99 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a Akure, babban birnin jihar, a ƙarshen mako, an kama shi ne a lokacin da yake ƙoƙarin jefar da gawar ƙaninsa da ya kashe.

  • Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
  • Kofin Duniya: FIFA Ta Fitar Da Yadda Za A Samu Gurbin Zuwa Amurka

Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Adebowale Lawal, ya bayyana cewa: “A ranar 26 ga watan Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 3 na rana, wani mutum mai suna Oluwafemi Oladipupo na titin Paragon, Kajola, ya kai rahoto a ofishin ƴan sanda na Kajola cewa ya lura da wani duro na roba mai launin shuɗi a gaban gidansa, da aka ɗaure bakinsa da igiya baƙa.”

“Bayan an buɗe duro ɗin, sai aka gano gawar wani matashi mai suna Otu Ifeanyi, mai shekara 18, wanda daga baya aka tabbatar shi ne ƙaninsa wanda ake zargi, a ciki. An gano duro ɗin ne a kan babur da wani mutum mai suna Eze Elechi Amadi yake tuƙawa. Yayin da yake ƙoƙarin kai duro ɗin zuwa wani wurin da ba a sani ba domin jefar da shi, sai ya zame daga kan babur ɗin ya fāɗi.”

Kwamishinan ƴan sanda na Jihar Ondo, Adebowale Lawal, ya bayyana cewa: “An kama wanda ake zargin nan take. A lokacin da ake masa tambayoyi, ya amsa cewa shi ne ya kashe ƙaninsa saboda rikicin kuɗi, inda ya zargi marigayin da tura Naira 20,000 daga asusun bankin Ecobank ɗinsa ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

“An ajiye gawar a ɗakin ajiye gawarwaki yayin da bincike ke ci gaba. Za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala binciken.”

Da yake magana kan sauran masu laifi da aka kama a faɗin ƙananan hukumomi 18 na jihar, kwamishinan ya ce an cafke su ne bisa zargin aikata laifuka da suka haɗa da: kisan kai, garkuwa da mutane, fashi da makami, shiga ƙungiyoyin asiri, mallakar miyagun ƙwayoyi ba bisa doka ba, da sata, da sauransu.

Lawal ya nuna cewa an samu nasarar waɗannan kame ne ta hanyar ƙoƙarin jami’an rundunar da kuma haɗin kan jama’ar jihar, waɗanda suka bayar da sahihan bayanai ga rundunar.

A cewarsa: “A cikin makonnin da suka gabata, rundunarmu ta samu nasarori wajen hana aikata laifuka, gano su, da kuma gurfanar da masu laifi a kotu. Waɗannan nasarori sun nuna ba wai kawai jarumtakar jami’anmu ba, har ma da haɗin kai mai daraja daga mutanen Jihar Ondo”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KisaTsrao
ShareTweetSendShare
Previous Post

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Next Post

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Related

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

15 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

6 days ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

6 days ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

1 week ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Tsaro

An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

2 weeks ago
Next Post
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.