• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

by Sani Anwar
1 day ago
in Labarai
0
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko shakka babu, tsarin tantance lafiya kafin a kai ga yin aure, yana da matuƙar amfani a tsanin al’umma.

Ya kamata a lura da cewa, idan aka gano guda daga cikin masu shirin yin aure yana ɗauke da wannan cuta, ba fa auren ake fasa yi ba, illa kawai dai za a ɗora shi a kan magani ne na tsawon wani lokaci, sannan kuma da zarar ya warke daga wannan ciwo na hanta, sai a ɗaura auren.

Daga cikin dalilan saukar da shari’a, akwai batun kiyaye lafiya. Saboda da haka, wannan tsari na tantance lafiya kafin aure; ya kamata ya zama wajibi a kan kowa da kowa.

dan guda daga cikin ma’aurata yana ɗauke da wannan cuta ta hanta, zai iya harbin aboki ko abokiyar zaman tasa; ba tare da ya sani ba, wannan shi ita ce babbar hikimar yin gwaje-gwaje a tsakanin masu shirin yin aure, kafin su kai ga yi.

  • Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
  • Yadda Ake Hada Miyar Hanta

Don haka, hanyoyin da ciwon hanta ke yaɗuwa sun haɗa da:

Labarai Masu Nasaba

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

1- Musayar yawu ta hanyar sumbatar juna- Ma’ana, ta hanyar sumbatar juna a tsakanin ma’aurata, idan guda daga cikinsu na ɗauke da cutar, nan da nan ɗayan shi ma zai kamu da cutar.

2- Gaurayewar jini ko haɗuwar jini- Haɗuwar jini, misali; idan wani ya yi amfani da reza ya yanke, ɗayan ya yi amfani da ita, zai iya kamuwa da cutar, ko kuma wani abu maikama da haka.

3- Ɓangaren saduwa a tsakanin ma’aurata- A wajen saduwa tsakanin mata da miji, ta hanyar haɗuwa maniyyi ko maziyyi da sauran makamantansu, wannan cuta za ta samu hanyar shigewa nan take da ɗaya daga cikinsu na ɗauke da ita.

Don haka, waɗannan hanyoyi da aka ambata dukkanninsu na iya faruwa a zamantakewar aure, kamar yadda masana kiwon lafiya suka sanar.

Saboda haka, ya zama wajibi mutane su kiyaye tare da bin ƙa’idojin waɗannan masana, musamman ta fuskar aiwatar da gwaje-gwaje, kafin a kai ga yin aure.

Wajibi ne ka kiyaye tare da kula da lafiyarka da kuma ta iyalinka, domin kuma sai an tambaye ka a kan yadda ka kula da ita. Sannan, yin wannan gwaji ba wani kayan gabas ba ne, duk da cewa; wasu na nuna tsoronsu a fili wajen zuwa a gwada su, wai a cewarsu; suna zaman-zamansu ka da ce; ba su da lafiya.

A nan, irin abin da Bahaushe yake cewa ne, “An gudu, ba a tsira ba”. Don haka, tun wuri kafin ku kai ga yin aure, ku je kai da yarinyar da za ka aura a gwada ku, a tabbatar da kwa ɗauke da wannan cuta ta hanta.

Haka nan kuma, su ma sauran ma’aurata; da zarar guda daga cikinsu, ya ji alamu ko an tabbatar masa da yana ɗauke da wannan cuta, ya yi ƙoƙarin taimaka wa abokin zaman nasa, ta hanyar zuwa yin gwaje-gwaje da kuma yin rigakafin kamuwa da cutar.

Mutane da dama, ba su san cewa; ana yin rigakafin wannan cuta ba, wanda abu ne da aka jima ana yi; ba lallai sai wanda ya kamu da cutar ba, kowa ma zai iya zuwa a yi masa kamar yadda masu iya magana ke cewa; “Rigakafi ya fi maganai”. 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hanta
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Next Post

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Related

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna
Labarai

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

10 hours ago
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

14 hours ago
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

16 hours ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

17 hours ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

17 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

18 hours ago
Next Post
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.