• English
  • Business News
Thursday, October 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
12 minutes ago
in Manyan Labarai
0
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata mata mai matsakaicin shekaru ta cinna wa kanta da kanta wuta a cikin gidan Firaministan Nijeriya na farko, marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa, da ke Bauchi, lamarin da ya janyo ajalinta.

 

Ganau sun ce akwai yiyuwar matar na fama da taɓin hankali wacce ta je gidan a cikin Keke-Napep ɗauke da galan ɗin man fetur.

  • Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

An labarto cewa ta je gidan ne da nufin ta ga Hajiya Yelwa Abubakar Balewa, ɗiyar Firaministan wacce kuma ita ce shugaban hukumar kula da marayu da marasa galihu ta jihar Bauchi (BASOVCA).

 

Labarai Masu Nasaba

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Ganau sun ƙara da cewa a lokacin da aka shaida wa matar cewa Yelwa ba ta nan, sai ta koma mashigar gidan ta kwarara wa kanta man fetur tare cinna ashana wanda hakan ya janyo wuta ta tashi.

 

Nan take lamarin ya janyo hankalin mutanen da suke kusa da wurin inda suka yi ƙoƙarin kashe wutar amma lamarin ya ƙazanta.

 

Daga baya kuma aka kwasheta zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), inda daga bisani ta rasu sakamakon ƙonewar da ta yi.

 

An kuma ce marigayiyar ɗiyar tsohon wani alkalin kotun Shari’a a Bauchi ce, wacce ta taɓa yin aure har da ‘ya’ya.

 

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil a ranar Alhamis ya tabbatar da faruwar lamarin tare da misalta hakan a matsayin abun takaici.

 

Ya ce Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci babban Baturen ɗansanda na cajin ofis ɗin ‘A’ Division da ya gudanar da bincike kan lamarin.

 

A cewar Wakil, binciken farko-farko ya nuna cewa matar na da tarihin matsalar ƙwaƙwalwa, wacce ta samu hakan tun lokacin da ta haihu na ƙarshe.

 

“An samu nasarar cetota a raye kuma an kaita Uwa je da ita asibitin tana raye ATBUTH, har an ɗaurata kan magani kafin daga bisani rai ya yi halinsa. Muna miƙi ta’aziyyarmu ga iyalanta da addu’ar Allah ya mata raham,” PPRO ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

Next Post

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Related

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

2 hours ago
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus
Manyan Labarai

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kama Ɓarayi A Jihar Neja

5 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

6 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Aukuwar Ambaliya A Wasu Jihohi

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi

19 hours ago
Next Post
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

October 2, 2025
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

October 2, 2025
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

October 2, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta  Barazana Ce Ga Makomar Nijeriya – Obasanjo

October 2, 2025
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kama Ɓarayi A Jihar Neja

October 2, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

October 2, 2025
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Aukuwar Ambaliya A Wasu Jihohi

October 2, 2025
Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.