• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NDLEA

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), reshen Jihar Bayelsa ta yi ƙawance da takwararta ta yaƙi da sha da safarar miyagun ƙwayoyi ta NDLEA domin tabbatar da an fatattaki masu safarar ƙwaya da baƙin-haure a jihar.

Kwanturolan reshen Jihar Beyelsa na NIS, James Sunday ya amshi baƙoncin takwaransa na hukumar yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi (NDLEA), Barista Mathew Ewa a ofishinsa da ke Yenagoa, kan wannan sabon yunƙurin nasu.

Hukumar NIS ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 7 ga watan Satumbar 2023, wanda jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ya rattaba wa hannu.

Sanarwar ta ce lokacin wannan ziyarar, Kwamandan NDLEA ya bayyana cewa hukumarsa za ta ƙaddamar da shirin yaƙar ta’ammuli da miyagun ƙwayoyi da kakkave baƙin haure a Jihar Bayelsa, wanda za su gudanar tare da NIS, idan Shugaban hukumar NIS, Isah Idris Jere ya amince. Haka kuma shirin zai gudana ne tare da haɗin kan Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri da sauren jami’an tsaro da ke Jihar Bayelsa.

Kwamandan ya ƙara da cewa za su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran hukumomin tsaro a jihar wajen samun nasarar wannan shirin, wanda zai tsaftace jihar daga korarowar baƙin haure da masu ta’ammuli da miyagun ƙwaroyi ta hanyar bin ƙa’idogin ECOWAS idan da buƙatar hakan.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

NDLEA
Hoto na gaba daya tsakanin jami’an NIS da takwarorinsu na NDLEA reshen Jihar Bayelsa

Sanarwr ta ce hukumar NIS ce za ta jagoranci shirin a wani vangare na gudanar da aiki a lokaci bayan lokaci tare da tilasta wa mazauna jihar wajen bin doka ta yadda baƙin haure ba za su karya dokokin Nijeriya da na ECOWAS na shige da fice a tsakanin mambobin ƙasashen ba.

Ta ce idan aka samu duk wani mazaunin jihar da hannu wajen gudanar da kasuwancin da ya sava da dokokin Nijeriya da na ECOWAS tare da haɗa baki da baƙin haure a lokacin wannan shirin, za a hukunta shi daidai da laifinsa kamar yadda doka ta tanada.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya

Matsalar Karancin Iskar Gas Na Addabar Turai Yayin Da Amurka Ke Kulla Makarkashiya

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.