• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Sanda 3, Fararen Hula 3 A Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Sanata Ubah

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Kashe ‘Yan Sanda 3, Fararen Hula 3 A Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Sanata Ubah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane shida da suka kunshi har da ‘yansanda uku da fararen hula uku ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da aka kai wa tawagar Sanatan da ke wakiltar mazabar Anambra ta Kudu, Sanata Ifeanyi Ubah.

Wasu ‘yan bindigan da ba a san ko su waye ba a ranar Lahadi sun farmaki tawagar Sanatan yankin Enugwu-Ukwu da ke karamar hukumar Njikoka a jihar Anambra.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in NSCDC Tare Da Garkuwa Da Mutum 3 A Ekiti

LEADERSHIP ta labarto cewa hamshakin mai hada-hadar Mai wanda shine mamallakin kamfanin Capital Oil and Gas, yana kan hanyarsa ta dawo daga cocin Anglican Synod a Ozubulu da ke karamar hukumar Ekwusigo zuwa wani otel din da ke zaune a Awka ne ‘yan bindigan dauke da muggan makamai farmaki tawagar a daidai Enugwu-Ukwu.

Kamar yadda ganau suka shaida, harin ya wakana ne da karfe 5 na yammacin ranar Lahadi. An ce Sanatan ya tsallake rijiya da baya ne sakamakon yana cikin mota wacce harsashi baya iya ratsata.

“Ba za mu iya ce ga kalar wadanda suka kawo harin nan zuwa yanzu ba. Kuma babu wanda ya san dalilin kai harin, amma kila ya kasance domin siyasa ko don harkarsa ta kasuwanci, za a iya tunanin komai,” a cewar majiyar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Kan wannan lamarin, cikin gaggawa gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya yi Allahwadai da harin tare da tabbatar da cewa wadanda suka kai farmakin ba za su sha haka nan ba dole sai sun dandana kudarsu kuma sai doka ta yi aiki a kansu.

Ya ce, wannan harin zai sanya su kawo karshen ayyukan ta’addanci a jihar.

Sakataren yada labarai na Soludo, Mr Christian Aburime, ya nakalto cewa gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga Sanata Ubah da kwamishinan ‘yansandan jihar CP Echeng Echeng, bisa rashin jami’ai da suka yi sakamakon harin.

Kazalika, daya daga cikin manyan masu kalubalantar kujerar Sanatan a zaben 2023, Kuma Dan takarar Sanatar mazabar na jam’iyyar APGA, Hon. Chris Emeka Azubuogu, ya yi tir da harin da aka kai wa Ubah ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamnan Jihar ba zai yi sako-sako da wannan lamarin ba har sai an hukunta masu hannu a lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Wadanda Suka Mutu Sakamakon Girgizar Kasa Mai Karfin Maki 6.8 Da Ta Afku A Lardin Sichuan Ya Kai 93

Next Post

Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

6 minutes ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Tinubu
Labarai

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

12 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

13 hours ago
Next Post
Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

Ministan Najeriya Ya Yi Maraba Da Kamfanonin Sin Da Su Zuba Jari A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.