• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Dan Takarar Sanata Na PDP Kan Amfani Da Takardun Bogi A Bayelsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Cafke Dan Takarar Sanata Na PDP Kan Amfani Da Takardun Bogi A Bayelsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansanda ta cafke tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bayelsa kuma dan takarar kujerar Sanatan Bayelsa ta tsakiya a zaben 2023 na jam’iyyar PDP, Hon. Friday Konbowei Benson, bisa zargin takardar bogi.

Benson, wadda tsohon sakataren Gwamnatin jihar ne, a lokacin zaben fitar da gwani na jam’iyyar PDP ya kayar da sanatan da ke kan a wannan kujerar na Sanatan mazabar Bayelsa ta tsakiya, Moses Cleopas da kuri’u 110.

  • PDP Ta KarÉ“e Ofisoshin YaÆ™in ZaÉ“en Buhari A Katsina

Cleopas dai bai ji dadin zaben fitar da gwanin da ya kai ga kayar da shi ba, inda ya dauki matakin kai karar Benson a gaban babban kotun tarayya da ke Yenagoa inda ke zarginsa da gabatar da takardun bogi ga hukumar zabe ta kasa INEC.

LEADERSHIP ta gano cewa jami’an ‘yansanda masu aiki a ofishin Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya a ranar Laraba sun yin dirar mikiya a Yenagoa babban birnin jihar Bayelsa tare da cafke Benson.

An ce sun dauke shi zuwa sashin binciken manyan laifuka (SCID) da ke jihar inda za a dauki bayansa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Kwamishinan ‘Yansandan Jihar, CP Ben Okolo ya tabbatar da cewa tawagar jami’ai daga ofishin IGP sun je jihar, sai dai ya ce bai da masaniya kan binciken da suke yi a jihar.

A lokacin da aka tuntubi Sanata Cleopas ta wayar tarho ya karyata cewa yana a hannu wajen ingiza ‘yansandan cafke abokin hamayyarsa.

“Rundunar ‘yansandan Nijeriya ba a karkashin ikona suke ba, don haka, ba ni ke da damar sanyasu su gudanar da aikin da ke gabansu. Suna gudanar da aikinsu ne,” ya ce.

Dangane da cewa ko korafin da ya shigar a kan Benson ne ya kai ga kama ma shi, sai ya ce yana da ikon rubuta korafin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Wasu Masu Fyade 4 Hukuncin Daurin Rai-Da-Rai A Jigawa

Next Post

Mahaifiyar Gwamnan Ondo, Grace Akeredolu, Ta Rasu Tana Da Shekaru 90

Related

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

2 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

6 hours ago
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina
Labarai

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

7 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

8 hours ago
Labarai

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

18 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

18 hours ago
Next Post
Mahaifiyar Gwamnan Ondo, Grace Akeredolu, Ta Rasu Tana Da Shekaru 90

Mahaifiyar Gwamnan Ondo, Grace Akeredolu, Ta Rasu Tana Da Shekaru 90

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.