• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daftarin Da Ya Shafi Jihar Xinjiang Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Daftarin Da Ya Shafi Jihar Xinjiang Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar kare hakkin bil Adama ta MDD, ta yi watsi da wani daftari da ya shafi jihar Xinjiang, wanda wakilin Sin ya bayyana a matsayin wani yunkuri na amfani da hukumomin kare hakkin dan Adam, domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Sin, da amfani da batutuwan da suka shafin Xinjiang domin dakile ci gaban kasar.

Chen Xu, shugaban tawagar kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva ne ya bayyana haka, inda ya ce Amurka da wasu kasashe ne suka shirya tare da gabatar da daftarin, suka kuma mika shi a matsayin matsalar dake bukatar gyara, a yunkurinsu na gaskata nazarinsu da ya sabawa doka, da sanya batutuwan da suka shafi Xinjiang da babu su a zahiri, a cikin ajandar majalisar.

  • Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Dakin Adana Kayan Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin Ta Samar

Ya bayyana gabanin kada kuri’a a jiya Alhamis, a zama na 51 na majalisar kare hakkin bil Adama cewa, batutuwan da suka shafi Xinjiang, ba su da alaka ko kadan da na hakkokin dan Adam, yana mai cewa, batutuwa ne da suka shafi yaki da ta’addanci da ra’ayi mai tsauri da kuma yaki da ‘yan aware.

Ya kuma shaidawa majalisar cewa, bisa namijin kokarin da aka yi, ba a samu ayyukan ta’addanci a Xinjiang ba, cikin shekaru 5 a jere. Kuma ana ba da cikakkiyar kariya ga hakkokin dukkan kabilun dake jihar.

A cewar Chen Xu, cikin sama da shekaru 60 da suka gabata, yawan al’ummar Uygur na Xinjiang ya karu daga miliyan 2.2, zuwa kusan miliyan 12, kuma matsakaicin shekarunsu na rayuwa ya karu daga 30 zuwa 74.7.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Ya ce ta hanyar yin biris da shaidu da gaskiya, Amurka da sauran wasu kasashe sun shirya tare da yada karairayi da jita-jita, a yunkurinsu na bata sunan Sin da kawo cikas ga zaman lafiya a jihar Xinjiang da dakile ci gaban kasar. Ya ce wannan misali ne na kulli irin na siyasa da take hakkin dan Adam mai tsanani, na dukkan kabilun jihar Xinjiang.

Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin ya bayyana a jiyan cewa, shaidu sun nuna sau da dama cewa, siyasantar da batun hakkin dan Adam, da nuna fuska biyu, ba za su yi tasiri ba, kuma yunkurin amfani da batutuwan da suka shafi jihar Xinjiang domin durkusarwa ko dakile kasar Sin ba zai yi nasara ba. (Fa’iza Msutapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Next Post

Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

17 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

18 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

19 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

20 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

21 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

22 hours ago
Next Post
Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.