• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karshen wannan makon ne, aka kammala babban taron wakilan JKS na 20,bayan shafe kwanaki bakwai ana tattauna.

Bayan kammala taron ne kuma babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci sauran shugabannin don ganawa da manema labarai na cikin gida da na waje, inda ya bayyana sabuwar alkiblar da kasar ta dosa, da yadda duniya za ta amfana daga jerin matakan da aka tsara aiwatarwa.

  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Kamar yadda kasar Sin ta sha bayyanawa, a wannan karon ma, babban sakatare Xi ya kara nanata kudirin kasar Sin na samar da gudummawa ga sauran kasashen duniya wajen samun ci gaba, kuma bunkasuwar kasar Sin za ta yi tasiri ga duniya baki daya. A gabar da kasar ta kama hanyar zamanantar da kanta.

Babban taron wata hanya ce ta kara daga tutar JKS, da hada karfi da karfe, da inganta hadin kai da sadaukarwa, don kara yiwa jama’a hidima da ma dogara da jama’a, da ci gaba da yin gyare-gyaren da suka dace da sabon tafarkin da aka sanya a gaba, sabanin yadda wasu jam’iyyun siyasa a kasashen yamma ke kara cusa jama’arsu cikin halin kunci, sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da yaduwar annobar COVID-19 da nuna wariya da sauransu.

Batun kara bude kofarta ga kasashen ketare, da sa kaimi ga zurfafa yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga waje a dukkan fannoni, bai sauya ba.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kuma ana iya ganin sakamakon haka, daga alkaluman da hukuma ta fitar dake nuna cewa, cinikayyar kayayyaki na ketare na kasar Sin, a cikin watanni 9 na farkon shekarar 2022 da muke ciki, ya karu da kashi 9.9 cikin 100, zuwa kudin Sin RMB Yuan triliyan 31.11, kwatankwacin dalar Amurka triliyan 4.75.

A cikin wannan wa’adi, cinikayyar kasar Sin da kasashen dake aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya karu da kashi 20.7 cikin 100 kan makamancin lokaci na bara, zuwa Yuan triliyan 10.04.

Wannan yana kara tabbatar da cewa, tattalin arzikin kasar Sin yana da juriya da kuma dama mai kyau, kuma tushen sa mai karfi ba zai taba sauyawa ba, zai kuma ci gaba da kasancewa bisa yanayi mai kyau da inganci na dogon lokaci.

Don haka, kasar Sin mai wadata, za ta kara samar da damammaki ga duniya baki daya. Kuma kamar yadda kasar Sin ba za ta iya samun ci gaba ita kadai ba, haka ma duniya tana bukatar kasar Sin wajen samun bunkasuwarta.

Masana daga sassan daban-daban na nahiyar Afirka wadanda ke zama kawaye kuma aminan kasar Sin, su ma sun bayyana cewa, taron yana da babbar ma’ana, wanda zai haifar da babban tasiri ga kasar Sin, da kara kuzari ga kasashen duniya wajen yin hadin gwiwa don tinkarar kalubale da samun bunkasuwa tare.

Nasarorin da kasar Sin ta cimma a aikin zamanintar da kanta bisa tsarinta, sun karfafa gwiwar kasashen duniya musamman ma kasashe masu tasowa, wannan zai baiwa sauran kasashe masu tasowa damar zabar dabarun raya kasashensu dake dacewa da yanayinsu. Kowa ne tsuntsu dai kukan gidansu ya ke yi.

Masu fashin baki na fatan kasashen duniya za su koyi fasahohi da shirye-shiryen samun ci gaba na kasar Sin da kuma damar hadin gwiwa daga taron wakilan JKS karo na 20, ta yadda za a tafiyar da harkokin duniya da ma tinkarar kalubalen da duniya ke fuskanta tare. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum Miliyan 93.5 Ne Za Su Kada Kuri’a A Zaben 2023 – INEC

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

1 hour ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

2 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

3 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

4 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

5 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

6 hours ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.