• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘Yan Jarida Manema Labaru (Yobe Correspondents’ Chapel) a Jihar Yobe, ta bayyana daukar matakin raba gari da gwamnatin jihar ta hanyar kauracewa dukar dukkan labaran aikace-aikacen gwamnatin jihar.

Kungiyar, a sanarwar bayan taron gaggawa wanda ta gudanar a ranar Jumma’a, 28 ga watan Oktoba, 2022- mai dauke da sa hannun Shugabanta da Sakatare; Ahmad I. Abba da Micheal Oshomah, sun bayyana daukar matakin sakamakon cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta.

  • An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata
  • 2022 Taron Makon Likitoci: Kebbi Ta Yi Asarar Kwararrun Likitoci 10 Cikin Shekara Guda – NMA

Kungiyar ta ce ci matakin ya zo ne sakamakon tursasawa tare da cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta da rashin kallon kimar da gwamnatin jihar ke nuna wa mambobinta.

“Saboda a matsayinmu na daya daga cikin ginshikai hudu a mulkin dimukuradiyya, bangaren da ke aikin sanar da al’umma dukkan abubuwan da ke faruwa a Jihar Yobe.”

“Wanda babban abin takaici ne, ace yau sama da shekara daya amma babu dan jarida a jihar da yayi fira kai tsaye da Gwamna Mai Mala Buni, sannan wannan Kungiyar ba ta taba samun wata gayyata a hukumance daga mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Muhammed ba, kamar yadda aka saba yi a baya.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

“Wannan ya haifar da mummunan gibi kuma yayi tasiri ga ayyukan wakilan jaridun Nijeriya daban-daban wadanda ke aiki a jihar Yobe.”

“Wanda ya toshewa dukan ‘yan jaridu masu aikin yada labaru samun duk wata damar kaiwa ga Gwamna Mai Mala Buni.”

“Saboda irin yadda wannan abin takaici ke ci gaba da gudana a karkace, kuma duk da cewa tarihi, Gwamna ya taba rike shugaban kwamitin riko a jam’iyyar APC na kasa, inda ya shafe sama da shekaru 3 ya na ganawa da manema labarai a Abuja, da sauran sassan kasar nan, amma ya kasa ya tattauna da yan jaridu a jiharsa, duk da yadda al’ummar jihar suke kewar sanin manufofin gwamnatinsa, tsare-tsare tare da ayyukan da ya aiwatar a cikin wadannan shekaru da yayi a matsayin Gwamnan jihar.”

“Wanda hakan ya jawo kungiyar ta yanke shawarar cewa ilahirin mambobinta za su daina daukar duk wani labari ko sanarwar manema labaru wanda gwamnatin jihar Yobe ta fitar har sai abin da hali yayi.”

“Haka kuma, mambobin wannan Kungiyar suna kira ga shugabannin hukumomin tsaro a jihar Yobe da su wayar da kan jami’ansu su dena cin zarafin kafafen yada labarai.”

“Sannan kuma, mambobin wannan Kungiyar ta ga cewa ya zama dole ta dauki wannan muhimmin mataki a daidai wannan gaba, domin jawo hankalin dukkan masu ruwa da tsaki da hukumomin da suka dace, saboda su dauki kwakkwaran matakin da ya dace tare da magance matsaloli da barazanar da manema labaru ke fuskanta a jihar Yobe don gyara su cikin tsanaki.”

“A karshe, muna sake nanata cewa yan jarida masu aikin yada labaru a jihar Yobe suna sanar da jama’a tare da gwamnatin jihar Yobe cewa basu dauki wannan matakin domin ra’ayin kansu ba, face kawai sai don kasancewarsu a matsayin su na daga cikin ginshikan da ke taimakon ci gaba da dorewar mulkin dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya.”

“Har ila yau, yana da mahimmanci a lura cewa babban zabe mai zuwa yana da matukar muhimmanci a dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya, don haka kuskure ne duk wani yunkurin yiwa kafafe yada labaru bita-da-kulli.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaGwamnatin YobeKungiyaManema LabaraiRaba GariYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

Next Post

Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

8 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

9 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

16 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

16 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

19 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

20 hours ago
Next Post
Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.