• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin, Nasara Ce Ta Duniya Ba Kalubale Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin, Nasara Ce Ta Duniya Ba Kalubale Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lamuran da suka faru a duniya, sun nuna mana cewa, nasara da ci gaban duniya, sun dogara ne da hadin gwiwa da taimakekeniya da kuma moriyar juna tsakanin kasa da kasa. Don haka, kyashi ko adawa da ci gaban wata kasa, ba zai taba amfanawa duniya ba.

Yadda kasashen yammacin duniya ke alakanta kasar Sin da kalmar “barazana” ko “kalubale”, abun damuwa ne ga zaman lafiya da ci gaban duniya. Nasarar Sin, nasara ce ga daukacin duniya, bisa la’akari da yadda karuwar tattalin arzikinta ko nasarori ko fasahohi ko ci gabanta ke shafar duniya baki daya.

  • Tashar Sararin Samaniyar Sin Za Ta Kasance “Gida Cikin Sararin Samaniya” Ga Dukkanin Bil Adama

Yayin da suke tattaunawa a makon da ya gabata, sabon Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak da shugaban Amurka Joe Biden, sun bayyana cewa, za su hada hannu wajen magance “kalubalen kasar Sin”.

Shi ma sakatare janar na kungiyar tsaro ta NATO, Jens Stoltenberg, ya bayyana kasar Sin a matsayin barazana, yayin da yake neman Amurka ta kara taimakawa Ukraine a rikicinsu da Rasha.

Ba mu taba jin inda aka ce kasar Sin ta kitsa juyin mulki a wata kasa ba, haka ma ba mu taba jin cewa Sin ta yi mulkin mallaka ko ci da gumin wasu kasashe ba. Kasar Sin ba ta taba girke sojojinta a wata kasa da sunan kare kanta ba, har ila yau, ba mu taba jin inda aka ce ta yi kutse ko katsalandan cikin harkokin wata kasa ko cusawa wata kasa manufofinta ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

To ya aka yi ta zama barazana ko kalubale?
Ko kadan, bai kyautu wadannan shugabanni su rika ayyana Sin a matsayin barazana ba, domin hakan, bata suna ne, suna nema jan Sin cikin rikicin da su ne suka rura wutar ta. Neman dorawa Sin laifi, ba zai kawar da hankalin duniya daga ainihin wadanda ke da alhakin haifar da rikicin ba. Kasar Sin ba ta taba sauya matsayarta game da batun Rasha da Ukraine ba, wadda ita ce hawa teburin sulhu.

A ganina, yadda ake alakanta ta da barazana ko kalubale, ba komai ba ne face adawa da ci gabanta da nasarori da farin jininta a idon duniya, wanda kuma ta same su ne ta sahihiyar hanya.

Don haka, yunkurin shafa mata kashin kaji, ba zai haifar da komai ba illa bayyana ainihin masu laifi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

Next Post

Kumbon Dakin Gwaji Na Mengtian Ya Hade Da Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

16 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

19 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

20 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Kumbon Dakin Gwaji Na Mengtian Ya Hade Da Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin

Kumbon Dakin Gwaji Na Mengtian Ya Hade Da Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.