• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Aka Tattauna A Wajen Shawarwarin Ministocin Tsaron Sin Da Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Jiya Jumma’a 10 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar tsaron kasar Sin, Wu Qian, ya kira taron manema labarai a wajen shawarwarin Shangri-La ko kuma SLD a takaice a kasar Singapore, inda ya bayyana yadda aka gudanar da shawarwarin ministocin tsaron kasashen Sin da Amurka.

Wu ya ce, a yayin shawarwarin, ministan tsaron kasar Sin, Wei Fenghe, ya jaddada matsayin kasar Sin kan batun Taiwan, inda ya ce, Sin kasa ce daya tilo a duniya, kuma Taiwan wani yanki ne da ba za’a iya balle shi daga kasar Sin ba. Manufar kasancewar kasar Sin daya tilo a duniya, tushen siyasa ne na alakokin Sin da Amurka, kana, amfani da batun Taiwan don kawo cikas ga ci gaban kasar Sin ba zai kai ga nasara ba.

  • Sin Ta Sake Neman Amurka Da Ta Bayyana Yadda Take Girmama Yarjejeniyar Haramta Makamai Masu Guba

Minista Wei ya ce, kwanan baya, kasar Amurka ta sake sanar da cewa za ta sayar da makamai ga yankin Taiwan, al’amarin da ya sabawa manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, gami da ka’idojin sanarwar hadin-gwiwa uku na kasashen biyu, da lalata cikakken yankin kasar Sin da moriyar tsaronta, kana lamarin ya lalata dangantakar Sin da Amurka da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan. Kasar Sin ta nuna adawa gami da yin Allah wadai da irin wannan batu.

Wu Qian ya ce, minista Wei ya jaddada cewa, in dai akwai wanda ke yunkurin balle Taiwan daga kasar Sin, babu tantama rundunar sojan kasar Sin za ta mayar da martani don tona asirinsu, da kiyaye cikakken yankin na kasar Sin.

Wu Qian ya kara da cewa, dangane da batun tekun kudancin kasar Sin, minista Wei ya ce, kasashen dake wannan yankin, suna da niyya da hikima gami da kwarewa sosai wajen daidaita batutuwan da suka shafi tekun kudancin kasar Sin. Shisshigin da kasashen da ba na wannan yanki ba suka yi, shi ne ke kawo rashin tabbas. Ya dace kasar Amurka ta dauki matakai a zahiri don amfanawa zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tekun kudancin kasar Sin, maimakon rura wutar rikici da tunzurin neman haifar da fito-na-fito.

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

An kaddamar da shawarwarin Shangri-La (SLD) karo na 19 a kasar Singapore a jiya Jumma’a, inda memban majalisar gudanarwa na kasar Sin, wanda kuma shi ne ministan tsaron kasar, Wei Fenghe ya halarci shawarwarin, da halartar tattaunawa da takwaransa na Amurka, Lloyd Austin. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Jakadan Sin A Saliyo Ya Halarci Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Ofishin Jakadancinsa Da Kungiyoyin Sada Zumunta Ta Kasashen Biyu

Jakadan Sin A Saliyo Ya Halarci Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Ofishin Jakadancinsa Da Kungiyoyin Sada Zumunta Ta Kasashen Biyu

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.