• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansanda Ta Karyata Rahoton Kai Wa Ayarin Motocin Atiku Hari A Jihar Borno

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Rundunar ‘Yansanda Ta Karyata Rahoton Kai Wa Ayarin Motocin Atiku Hari A Jihar Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta karyata rahoton harin da aka kai kan ayarin motocin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, a yayin gangamin yakin neman zabe a Maiduguri, babban birnin jihar Borno a ranar Laraba.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Abdu Umar ne ya bayyana hakan ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), Sani Shatambaya, wanda ya bayyana labarin a matsayin labaran karya da masu neman yada fitina suka yada musamman a shafukan sada zumunta.

  • ‘Yandaba Sun Farwa Tawagar Atiku Farmaki, Mutum 74 Sun Jikkata Suna Asibiti A Borno

Shatambaya ya ce, “Kwamishanan ‘yan sanda mai kula da rundunar ‘yan sandan jihar Borno, CP Abdu Umar, yana so ya jaddada cewa ba a kai wa ayarin motocin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP hari ba a yayin gangamin yakin neman zaben da aka gudanar a jihar a ranar 9 ga Nuwamba, 2022.

Atiku
Wani bangare na mahalarta taron yakin neman zaben da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya gudanar a ranar 9 Nuwamba, 2022 a Jihar Borno

“An gudanar da yakin neman zaben cikin nasara, sabida an dauki tsauraran matakan tsaro a duk lokacin da ake gudanar da ayyukan, an baza jami’an tsaro ta ko’ina a yayin gangamin, sai dai, an kama wani Danladi Musa Abbas mai shekaru 32 a lokacin da ake gudanar da gangamin da laifin haifar da wani dan karamin rikici a hanyar airport road, sai wasu masu yada jita-jita suka kara ta’azzara rahoton hakan kamar yadda ake ta yadawa.

“Sabida haka, kwamishinan ‘yan sanda, CP Abdu Umar, ya yi kira ga sauran jama’a da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a jihar da su daina yada labaran karya da za su iya kawo cikas ga zaman lafiyan da ake samu a jihar, musamman ganin yadda babban zaben 2023 ke gabatowa.”

Labarai Masu Nasaba

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Next Post

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Related

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

20 minutes ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

3 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

5 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

7 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

18 hours ago
Next Post
Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.