ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansanda Ta Karyata Rahoton Kai Wa Ayarin Motocin Atiku Hari A Jihar Borno

by Sulaiman
3 years ago
Atiku

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta karyata rahoton harin da aka kai kan ayarin motocin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, a yayin gangamin yakin neman zabe a Maiduguri, babban birnin jihar Borno a ranar Laraba.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Abdu Umar ne ya bayyana hakan ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), Sani Shatambaya, wanda ya bayyana labarin a matsayin labaran karya da masu neman yada fitina suka yada musamman a shafukan sada zumunta.

  • ‘Yandaba Sun Farwa Tawagar Atiku Farmaki, Mutum 74 Sun Jikkata Suna Asibiti A Borno

Shatambaya ya ce, “Kwamishanan ‘yan sanda mai kula da rundunar ‘yan sandan jihar Borno, CP Abdu Umar, yana so ya jaddada cewa ba a kai wa ayarin motocin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP hari ba a yayin gangamin yakin neman zaben da aka gudanar a jihar a ranar 9 ga Nuwamba, 2022.

ADVERTISEMENT
Atiku
Wani bangare na mahalarta taron yakin neman zaben da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya gudanar a ranar 9 Nuwamba, 2022 a Jihar Borno

“An gudanar da yakin neman zaben cikin nasara, sabida an dauki tsauraran matakan tsaro a duk lokacin da ake gudanar da ayyukan, an baza jami’an tsaro ta ko’ina a yayin gangamin, sai dai, an kama wani Danladi Musa Abbas mai shekaru 32 a lokacin da ake gudanar da gangamin da laifin haifar da wani dan karamin rikici a hanyar airport road, sai wasu masu yada jita-jita suka kara ta’azzara rahoton hakan kamar yadda ake ta yadawa.

“Sabida haka, kwamishinan ‘yan sanda, CP Abdu Umar, ya yi kira ga sauran jama’a da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a jihar da su daina yada labaran karya da za su iya kawo cikas ga zaman lafiyan da ake samu a jihar, musamman ganin yadda babban zaben 2023 ke gabatowa.”

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Next Post
Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.