• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Amince Da Kafa Asusun Tallafawa Kasashe Masu Tasowa Da Kudaden Yaki Da Tasirin Sauyin Yanayi Yayin Taron COP27

by CMG Hausa
3 years ago
COP27

Kasashe mahalarta taron COP27 da ya kammala a jiya Lahadi, sun amince da kafa wani asusun musamman, wanda zai tattara kudaden tallafawa kasashen da ke fuskantar barazanar sauyin yanayi, ta yadda za su iya tunkarar ayyukan yaki da tasirinsa yadda ya kamata.

Taron na bana, shi ne na 27 da kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD ko UNFCCC suka gudanar, kuma cikin wata sanarwa da ya fitar game da hakan, babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya yi na’am da kafa asusun, wanda zai samar da diyyar asara da lalacewar muhalli, yana mai fatan asusun zai yi aiki yadda ya kamata.

  • Wang Yi: Ziyarar Xi A Ketare Na Nuni Da Yadda Sin Ta Himmatu Wajen Samun Ci Gaban Duniya

Mr. Guterres ya kara da cewa, taron na makwanni biyu da ya gudana a birnin Sharm El-Sheikh na kasar Masar, ya zamo wani ginshiki mai muhimmanci na tabbatar da adalci. Sai dai kuma ya ce kudaden da ake fatan tarawa ba za su isa ba, ko da yake tara kudin tamkar tabbatar da aniyar siyasa ce da za ta sake gina amincin da ya riga ya gurgunce.

A nasa bangare kuwa, yayin wata zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, shugaban tawagar kasar Sin a taron na COP27, kuma mataimakin ministan muhalli da muhallin halittu na Sin Zhao Yingmin, cewa ya yi taron na COP27 ya yi rawar gani, wajen zakulo matakan jure sauyin yanayi, da tattara kudade na diyyar asara da lalacewar muhalli, wadanda su ne manyan abubuwan damuwa ga kasashe masu tasowa.

Kaza lika Zhao ya ce a taron na bana, kasashe masu wadata sun fito da muhimman batutuwa da suka dace, kamar batun samar da kudade, da tallafin kwarewa da kasashe masu tasowa ka iya cin gajiyar su, suna fatan kasashe masu wadata za su yi aiki tare da sauran sassan kasa da kasa, wajen gina yanayi mai dorewa domin gobe.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Tun da farko, wakilin musamman na kasar Sin game da sauyin yanayi Xie Zhenhua, ya yi kira ga kasashe masu sukuni, da su ba da gudummawa, ga cimma nasarar kudurin dake kunshe cikin yarjejeniyar Paris, ta hanyar kafa asusun diyyar asara da lalacewar muhalli, domin taimakawa kasashe masu tasowa, ta yadda za su shawo kan kalubalen sauyin yanayi.

Xie ya ce kasashe masu tasowa ne za su ci gajiyar asusun, kuma bisa la’akari da karancin kudaden dake cikinsa, kamata ya yi a fara da baiwa kasashe mafiya fama da kalubalen sauyin yanayi, da wadanda ke cikin matukar bukata. (Mai Fassarawa: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Taron MDD Da Sin Kan Huldar Kasa Da Kasa Game Da Binciken Sararin Samaniya

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Taron MDD Da Sin Kan Huldar Kasa Da Kasa Game Da Binciken Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.