A karon farko a matsayinsa na Shugaban kasar Amurka, Joe Biden zai kai wata ziyara yankin Gabas ta Tsakiya.
BBC ta wallafa a shafinta cewa, ana sa ran shugaban zai kai ziyara Æ™asashen Saudiyya da Isra’ila da kuma wasu yankunan Palestine.
Shugaban zai yi tafiyar ne a watan Yuli mai zuwa inda zai shafe kwana huÉ—u yana rangadi.
Mista Biden dai zai kafa tarihi a matsayinsa na Shugaban Amurka idan ya je Saudiyya daga Isra’ila – hanya ce ta jirgi da Saudiyya ba ta cika bari ana bi ba sakamakon rashin jituwa irin ta diflomasiyya tsakanin Isra’ila da Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp