• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Yi Jawabi A Yayin Bude Taro Zagaye Na 2 Na Yarjejeniyar COP15

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Yi Jawabi A Yayin Bude Taro Zagaye Na 2 Na Yarjejeniyar COP15
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta sanar da cewa, a gobe Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, yayin bude taro zagaye na biyu, na wakilan bangarorin da suka sanya hannu kan jarjejeniya kasancewar mabambantan halittu karo na 15 ko COP15.

Sannan, Shugaban taron MDD kan wanzuwar mabanbantan halittu, kuma ministan ma’aikatar kula da muhalli da muhallin halittu ta kasar Sin Huang Runqiu, ya yi kira ga sassa masu ruwa da tsaki da su tashi tsaye, wajen jajircewa, da nuna hikima da kwazo, domin toshe gibin dake akwai, da sabani, ta yadda za a cimma nasarorin da aka sanya gaba.

  • An Shirya Gudanar Da Kashi Na Biyu Na Taron COP15

Huang Runqiu ya yi tsokacin ne a jiya Talata, yayin taron manema labarai, karkashin taron sassan da suka amince da yarjejeniyar MDD game da wanzuwar mabanbantan halittu karo na 15 ko COP15 a takaice.

Huang ya kara da cewa, sakamakon rawar da daukacin sassan masu ruwa da tsaki a yarjejeniyar suka taka, taron ya cimma manyan nasarori.

Cikin su har da amincewa da shawarwari guda 23, wadanda suka kai kaso daya bisa uku na jimillar shawarwarin da ake bukata wajen cimma nasarar taron. Ya ce a wasu sassa masu muhimmanci ma, dukkanin bangarorin sun yin musayar ra’ayi mai zurfi kan matsayar su da mahangar su.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An bude taron game da yarjejeniyar MDD mai nasaba da wanzuwar halittu mabanbanta ne a makon jiya, kuma taron ya shiga lokaci mafi muhimmanci, yayin da ya rage mako guda a fitar da kundin da zai yi bitar matakan sauya asara, da koma-bayan da aka samu, game da wanzuwar mabanbantan halittu.

Bisa tanadin taron, za a gudanar da zaman dandalin ministoci tsakanin ranakun 15 zuwa 17 ga watan Disambar nan, domin warware batutuwa masu sarkakiya dake cikin kundin.
Da take tsokaci yayin taron manema labaran da ya gudana, babbar sakatariyar taron Elizabeth Maruma Mrema, ta ce “Muna bukatar wannan tattaunawa, domin cimma nasarar fitar da kyakkyawan tsari mai inganci, na gudanar da ayyukan da za su dakatar da asarar da ake tafkawa, a fannin wanzuwar halittu mabanbanta, tare da share fagen farfado da fannin yadda ya kamata”. (Safiyah Ma, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Mallakar Katin Zabe Ya Fi Mallakar Takardun Makaranta A Wannan Lokacin -Gumi

Next Post

Qatar 2022: Faransa Ta Doke Morocco A Wasan Zagayen Kusa Da Na Karshe

Related

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

1 hour ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

2 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

20 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

21 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

22 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

23 hours ago
Next Post
Qatar 2022: Faransa Ta Doke Morocco A Wasan Zagayen Kusa Da Na Karshe

Qatar 2022: Faransa Ta Doke Morocco A Wasan Zagayen Kusa Da Na Karshe

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.