• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Neman Ci Gaba Ta Hanyar Lumana Domin Amfanin Daukacin Bil Adama

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A yayin taron wakilan jamiyyar kwaminis ta kasar Sin JKS karo na 20 da ya gabata cikin shekarar da ta shude, shugaban kasar Xi Jinping ya taba alli game da yadda JKS ta shafe gwamman shekaru tun kafuwarta, tana aiki tukuru wajen tabbatar da nasarar bunkasa kasa ta hanyar lumana, da ingiza ci gaban rayuwar daukacin alummun duniya.

Ko shakka babu, ga duk mai bibiyar tarihi, ya kwana da sanin cewa, tashe-tashen hankula da yake-yake, ko zaman doya da man ja, wadanda suka wakana tsakanin kasashe daban daban, ba su taba haifar da da mai ido ba. Don haka ne ma shaidun gani da ido, ke dada tabbatar da muradun kasar Sin na bin hanyoyin zaman lafiya domin samun ci gaba, wanda hakan ya zama babban jigo a manufofin diflomasiyyar kasar.

  • Wang Yi Ya Jagoranci Taron Manyan Wakilai Game Da Nazarin Matakan Aiwatar Da Manufofin Taron Ministocin FOCAC Na 8

A mahangar kasar Sin, zaman lafiya da ci gaba, tamkar dan juma ne da dan jummai, wato dai muhimman tagwaye ne da ba za a iya raba su ba, don haka mahukuntan kasar ke kara kaimi ga dukkanin hanyoyin raya dangantaka da sauran sassan duniya cikin lumana. Alal misali, Sin ta gabatarwa duniya da shawarar nan ta “ziri daya da hanya daya”, da dandalin raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, ta kuma fadada jarin waje da take zubawa a kasashen Afirka, domin tallafa musu wajen bunkasa tattalin arzikinsu. Wadannan da ma karin wasu manufofin na samar da gata ga kasashe masu tasowa, sun sa akasarin sassan kasa da kasa na kallon kasar Sin a matsayin babbar kawa, kuma aminiyar huldar kasashe masu tasowa, musamman a fannonin samar da ababen more rayuwa, da cinikayya, da zuba jari da hadin gwiwar raya sassan tattalin arziki.

Bugu da kari, kasar Sin na goyon bayan gudanar da cudanyar dukkanin sassan kasa da kasa, da hada-hadar cinikayya maras shinge, da tsaron kasa da kasa, da ayyukan wanzar da zaman lafiya. Tana kuma kaucewa yin mummunar takara ko neman yin babakere, sabanin yadda wasu manyan kasashe musamman na yammacin duniya ke nacewa hakan.

Ko shakka babu, manufofin kasar Sin na wanzar da ci gaba ta hanyar lumana domin cin gajiyar daukacin bil adama, za su ci gaba da haifar da gajiya da dukkanin sassan kasa da kasa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. (Saminu Hassan)

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
Daga Birnin Sin

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
Daga Birnin Sin

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.