• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Fara Aikin Cibiyar Fasfo Ta Zamani A Ogun

byAbdulrazaq Yahuza
3 years ago
ogun

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da fara aikin gina katafariyar cibiyar samar da ingantaccen fasfo na zamani a Jihar Ogun da ke shiyyar kudu-maso-yammacin ƙasar nan.

Shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris ya jagorancin ƙaddamarwar yayin da ya kai wata ziyara ta musamman a jihar.

  • NIS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Kano

Da yake jawabi yayin ƙaddamarwar, Isah Jere ya ce ƙaddamar da aikin ta zo a kan gaɓa bisa himma da ƙoƙarin da NIS ke ci gaba da yi wajen bunƙasa ayyukanta ga ‘yan ƙasa cikin ƙwarewa.

ogun

“Wannan aiki da ake ƙaddamarwa a yau zai bunƙasa ayyukan bayar da fasfo a wannan jiha da ta kasance mashigi. Ina taya ‘yan asalin jihar da sauran ‘Yan Nijeriya murnar wannan ci gaba da aka samu saboda zai kawo musu sauƙi wajen samun biyan buƙata daga ayyukan da Babban Ofishin NIS na Jihar Ogun ke gudanarwa ga ‘yan ƙasa”.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

CGI Isah Jere ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar ta Ogun Adedapo Obiodun bisa samar da katafaren filin da za a gina cibiyar da kuma haɗin gwiwa da goyon bayan da NIS take samu tun a shekaru da dama daga Gwamnatin Ogun.

“Tabbas, Babban Ofishin NIS na Jihar Ogun yana cin gajiyar gudunmawa da goyon bayan da yake samu daga jihar kuma muna ƙara tsumayar ƙarin haɗin gwiwa a tsakaninmu.

Shugaban na NIS Isah Jere ya ziyarci fadar gwamnatin jihar da fadar babban basaraken Ogun a yayin ziyarar. Haka nan ya kai ziyarar gani da ido a wani kamfani na cikin gida, PROFORCE, da ke kera motoci masu sulke a Iperu da ke Jihar Ogun.

CGI Isah Jere Idris (a hagu) tare da tawagarsa yayin ziyara a Kamfanin PREFORCE

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Abuja Sun Kashe Wani Magidanci Da Sace ‘Ya’yansa 2

'Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Abuja Sun Kashe Wani Magidanci Da Sace 'Ya'yansa 2

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version