• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Nuna Sahihanci Ga Kasashen Afirka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na Nuna Sahihanci Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan wani abokinka yana zuwa gidanka don gaishe ka, da nuna fatan alheri a farkon duk wata sabuwar shekara, cikin shekaru 33 a jere. Shin kauna da sahihanci da ya nuna maka za su burge ka?

A kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya yi ziyara a kasashen Habasha, da Gabon, da Angola, da Benin, gami da Masar, wadda ta kasance ziyara ta farko da jami’in ya yi, bayan da ya hau mukamin ministan wajen kasar Sin. Kana ya zama shekaru 33 a jere, da ministan waje na kasar Sin ya kai ziyara a nahiyar Afirka a farkon duk shekara. Hakan ya shaida dadadden zumuncin da ake da shi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, da sahihancin da kasar Sin ta nuna ma abokanta dake nahiyar Afirka.

Wannan sahihanci, shi ne tushen hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ya tabbatar da yanayin hadin gwiwa na amfanar da juna, da haifar da ci gaba ga dukkan bangarorin kasashen Afirka da kasar Sin:

Tun daga shekarar 2000, kasar Sin ta gina layin dogo fiye da kilomita 6000, da hanyoyin mota na kilomita 6000, da tashoshin jiragen ruwa kimanin 20, da manyan tashoshin samar da wutar lantarki fiye da 80, a kasashen Afirka. Gami da ba da tallafin asibitoci fiye da 130, da makarantu fiye da 170, da dakunan wasannin motsa jiki 45, da ayyukan aikin gona fiye da 500 a nahiyar Afirka.

Kaza lika a kasuwannin kasar Sin, yanzu ana iya ganin gahawa, da kayayyakin hannu, da dai sauransu, wadanda aka samar da su a kasashen Afirka, wadanda suka taimakawa inganta zaman rayuwar Sinawa.

Labarai Masu Nasaba

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Yayin da minista Qin Gang ke ziyara a kasar Habasha a wannan karo, ya halarci bikin kammala ginin babbar cibiyar hana yaduwar cututtuka ta nahiyar Afirka. Wannan aiki shi ma ya shaida sahihancin da kasar Sin ta nuna ma kasashen Afirka.

Yayin barkewar annobar cutar Ebola a yammacin Afirka a shekarar 2014 ma, kasar Sin ta samar da tallafi ga kasashen da annobar ta shafa, da kungiyar kasashen Afirka ta AU, ba tare da jinkiri ba. Daga baya kuma, Sin ta sanar da samar da gudummawar gina ginin babbar hedkwatar cibiyar hana yaduwar cututtuka ta nahiyar Afirka kyauta, don tallafawa kokarin kasashen nahiyar na kare lafiyar jama’arsu.

Yanzu hakan dai an mika wa kungiyar AU, manyan bangarori na wannan babban gini wanda fadinsa ya kai muraba’in mita dubu 90, wanda aka kashe dalar Amurka miliyan 80 wajen gina shi. Wannan babbar kyauta ta nuna yadda kasar Sin take samar wa kasashen Afirka da hakikanin taimakon da ake bukata, ba tare da gindaya wani sharadi ba. Kana duk wani alkawarin da kasar Sin ta yi, to, za ta cika shi.

Ban da wannan kuma, ana iya ganin sahihancin da kasar Sin ta nuna, bisa yadda ta ki yarda da yunkurin siyasantar da batun hadin gwiwa da kasashen Afirka. A lokacin da yake hira da manema labaru, tare da shugaban kwamitin kungiyar AU Moussa Faki Mahamat, Mista Qin Gang ya ce, “Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, maimakon fagen takarar manyan kasashe. Idan dole ne a yi takara, to, ya dace a duba wace kasa ta fi samar da gudunmowa ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a nahiyar Afirka, gami da taimakawa kasashen Afirka, samun karin wakilci da ikon fada a ji a fannin kula da al’amuran kasa da kasa. ” A cewarsa, duk wata kasa, idan ta nuna sahihanci, na tabbatar da samun zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a nahiyar Afirka, to, kasar Sin za ta mara mata baya.

Hakika kokarin hadin gwiwa da kasashen Afirka da kasar Sin take yi, ya riga ya janyo karin jari zuwa nahiyar Afirka, daga kasashen yamma. Yayin da wani masani dan Najeriya mai suna Ovigwe Eguegu ke hira da manema labaru a kwanan baya, ya ce, manyan shirye-shiryen zuba jari na “Huldar abokai ta gina kayayyakin more rayuwa da zuba jari ko (PGII)” na kungiyar G7, da shirin “Kofofin duniya” (Global Gateway) na kungiyar tarayyar Turai na EU, an gabatar da su ne, bayan da aka ga yadda shirin “Ziri daya da hanya daya ko (B&R)” na kasar Sin ke yin muhimmin tasiri a duniya.

Sai dai kasashen yamma sun ki yarda da sahihancin kasar Sin, har ma kafofin watsa labarun su na cewa wai kasar Sin, ta jefa kasashen Afirka cikin “tarkon bashi”. Dangane da wannan zargi, Mista Qin Gang ya mayar da martani ta hakikanan bayanai.

A cewarsa, kasar Sin ta yi kokarin halartar shirin dakatar da biyan bashi karkashin laimar kungiyar G20, inda ta kulla yarjejeniya, ko kuma cimma ra’ayi tare da kasashe 19 dake nahiyar Afirka, a fannin dakatar da biyan bashi, lamarin da ya sanya kasar zama mafi samar da sakamako a wannan fanni, cikin mambobin kungiyar G20.

A sa’i daya kuma, wani rahoto daga bankin duniya ya nuna cewa, hukumomin hada-hadar kudi na kasa da kasa, da ‘yan kasuwa masu ba da bashi, suna rike da kashi 3 cikin kashi 4 na dukkan bashin da ake bin kasashen Afirka. Saboda haka Mista Qin ya bukaci wadannan hukumomi, da mutane da su kara taka rawa a fannin sassauta matsalar bashi a kasashen Afirka.

Hakika dalilin da ya sa kasashen yamma ba za su yarda da sahihanci na kasar Sin ba, shi ne domin akwai bambancin ra’ayi tsakaninsu. A ganin mutanen kasashen yamma, moriyar kai ta fi muhimmanci, amma tunanin da kasar Sin ta daukaka shi ne, kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. A ganin Sinawa, wasu manyan matsaloli sun shafi duniya baki daya, kana babu wata kasa da za ta iya kare kai, ba tare da hadin gwiwa da sauran kasashe ba. Saboda haka, ya kamata a lura da damuwar sauran kasashe, yayin da ake neman tabbatar da moriyar wata kasa, gami da ciyar da tattalin arzikin kasashe daban daban gaba, yayin da ake neman raya kai.

Wannan tunani shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin ke ta nuna cikakken sahihanci ga abokanta dake nahiyar Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burina

Next Post

A Boye DSS Ta Ayyana Cafko Emefiele – Femi Falana

Related

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

4 minutes ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

2 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

5 hours ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

6 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

8 hours ago
Next Post
Emefiele: Duk Mai Tunanin Sauro Ya Yi Kadan Bai Kwana Da Shi Ba Ne!

A Boye DSS Ta Ayyana Cafko Emefiele - Femi Falana

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.