• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarkon Bashi Na Shan Suka Daga Sassan Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
Tarkon bashi

Ga duk mai bibiyar kafafen watsa labaran yammacin duniya, da irin kalaman da kan fito daga bakunan manyan jamian Amurka, ba zai rasa jin zarge-zarge marasa dalili kan kasar Sin ba. Cikin wadanda suka fi fitowa fili, a baya bayan nan an ji zargin cewa wai kasar Sin na Danawa kasashen Afirka Tarkon Bashi. Kana a baya bayan nan ma, an jiyo sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen, na cewa wai Sin ta yiwa shirin tattaunawa game da lamunin da kasar Zambia ke karba kafar ungulu.

Idan muka bibiyi wannan kalamai na Janet Yellen, za mu ga ba su da tushe ko kadan, domin kuma su kansu mahukuntan kasar Zambia sun musanta hakan, suna masu bayyana kalaman da cewa sam ba su dace su fito daga bakin babbar jamiar Amurka ba. Har ma wasu masu fashin baki na cewa bai dace jamiar ta furta kalamai masu nasaba da alakar Sin da Zambia, yayin da take ziyarar aiki a Zambia ba, domin da farko ma hakan ya sabawa daar ayyukan diflomasiyya.

  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Sakon Bidiyo Ga Taron Koli Karo Na 7 Na Kungiyar Kasashen Latin Amurka Da Caribbean

Kaza lika, matsayar Sin game da bashin dake tsakaninta da Zambia a bayyane take, kasancewar Sin da Zambia kawaye ne na tsawon lokaci, kuma abokan hadin gwiwar samar da ci gaba. Ana iya shaida hakan, idan aka dubi yadda Sin ta tallafawa Zambia da kudaden gudanar da layin dogo da ya hada Tanzania da Zambia tun a shekarun 1970, lokacin da ita kanta Sin ba ta da cikakkiyar wadata.

Har ila yau a yanzu ma, Sin ta samar da kudaden aiwatar da manyan ayyukan raya kasa a Zambia, wanda hakan ke dada tabbatar da aniyarta ta ingiza ci gaban kasar.

Ko shakka babu, kalaman waccan jamia ta Amurka sun sabawa kaida, kuma akwai bukatar tsagin Amurka ya yi amfani da damarsa, ta inganta alaka da Zambia wajen gabatar da agaji na kara bunkasa kasar, maimakon mayar da Sin abun suka a idon sahihan kawayen ta na nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Wasu dai na kallon irin wadannan kalamai daga jamian Amurka, a matsayin kunna wutar yakin cacar baka, da nuna alamu na wata mummunar takara tsakanin ta da sauran kasashen duniya dake kawance da kasashen Afirka. Har ma wasu na cewa, idan har Amurka ba ta sauya matsa wajen kallon Sin a matsayin wata barazana ba, hakan na iya zama manuniya dake tabbatar da cewa, burin Amurka shi ne mayar da nahiyar Afirka fagen dagar takara, maimakon wuri da za a tallafawa ya samu ci gaban da yake fata, kuma nahiya da ke bukatar hadin kan dukkanin kasashen da suka ci gaba, ta yadda za a gudu tare a tsira tare! (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Ku Daina Bin Layin Bankuna, Ku Cire Kudi A Wajen Masu POS – CBN Ga Kwastomomi

Ku Daina Bin Layin Bankuna, Ku Cire Kudi A Wajen Masu POS - CBN Ga Kwastomomi

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.