• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasa da awa 48 kafin gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar Asabar, jam’iyyar APC a Jihar Ribas, ta soki mataimakin Sufeton ‘yansanda, AIG Abutu Yaro da Kwamishinonin ‘yansanda hudu da aka turo zuwa jihar domin sa ido kan zabe saboda ziyarar da suka kai wa gwamnan jihar, Nyesom Ezenwo Wike.

Kwamishinonin da suka hada da Yomi Olanrewaju, Samuel Musa, Lanre B. Sikiru da kuma Aderemi Adeoye.

  • Kungiyoyi Magoya Bayan Buhari-Osinbajo Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Zabi Atiku Na Jam’iyyar PDP
  • An Daure Dan Kamasho Wata 6 Kan Satar Batirin Mota A Abuja

Kakakin kwamitin yakin neman zaben APC a jihar Sogbeye Eli, a hirarsa da manema a yau Alhamis, ya ce, a bisa wannan ziyarar da suka kai wa Wike sun kasance ba su da wani kwarin guiwa a kan ‘yansanda.

Sogbeye ya ci gaba da cewa, Wike da ‘yan barandarsa sun kitsa yadda za su yi magudin zabe, inda ya ce, Wike ya fitar da miliyoyin Naira har da kudaden kasar waje ya raba wa jami’an.

A cewarsa, jami’an sun kuma kasance suna yin sintirin gidan Wike da dare da ke a yankin Rumuepirikom tun a ranar 22 ga watan Fabirairu 2023.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Kakakin ya kuma yi zargin cewa, Wike ya kitsa wani shiri da jami’in tsaro a jihar domin a yi wa shugabanin APC dauki dai-dai a jihar, har da na kananan hukomomi.

Ya sanar da cewa, “Mun samu bayanan sirri daga kananan hukomomin jihar cewa, ana son a dauke shugabanin APC da dama, don a tauye masu ‘yancinsu a lokacin gudanar da zabe.”

Ya buga misali da dauke Victory Agbara a karamar hukumar Tai a ranar 21 ga watan Fabirairu 2023, bayan ya fice daga PDP ya komawa jam’iyyar APC, inda kuma bayan kwana biyu, aka shigar da karar Ogbonna Nwuke a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCRibasSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

Next Post

Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

3 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

8 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

9 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

10 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

12 hours ago
Next Post
Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.