• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasa da awa 48 kafin gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar Asabar, jam’iyyar APC a Jihar Ribas, ta soki mataimakin Sufeton ‘yansanda, AIG Abutu Yaro da Kwamishinonin ‘yansanda hudu da aka turo zuwa jihar domin sa ido kan zabe saboda ziyarar da suka kai wa gwamnan jihar, Nyesom Ezenwo Wike.

Kwamishinonin da suka hada da Yomi Olanrewaju, Samuel Musa, Lanre B. Sikiru da kuma Aderemi Adeoye.

  • Kungiyoyi Magoya Bayan Buhari-Osinbajo Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Zabi Atiku Na Jam’iyyar PDP
  • An Daure Dan Kamasho Wata 6 Kan Satar Batirin Mota A Abuja

Kakakin kwamitin yakin neman zaben APC a jihar Sogbeye Eli, a hirarsa da manema a yau Alhamis, ya ce, a bisa wannan ziyarar da suka kai wa Wike sun kasance ba su da wani kwarin guiwa a kan ‘yansanda.

Sogbeye ya ci gaba da cewa, Wike da ‘yan barandarsa sun kitsa yadda za su yi magudin zabe, inda ya ce, Wike ya fitar da miliyoyin Naira har da kudaden kasar waje ya raba wa jami’an.

A cewarsa, jami’an sun kuma kasance suna yin sintirin gidan Wike da dare da ke a yankin Rumuepirikom tun a ranar 22 ga watan Fabirairu 2023.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Kakakin ya kuma yi zargin cewa, Wike ya kitsa wani shiri da jami’in tsaro a jihar domin a yi wa shugabanin APC dauki dai-dai a jihar, har da na kananan hukomomi.

Ya sanar da cewa, “Mun samu bayanan sirri daga kananan hukomomin jihar cewa, ana son a dauke shugabanin APC da dama, don a tauye masu ‘yancinsu a lokacin gudanar da zabe.”

Ya buga misali da dauke Victory Agbara a karamar hukumar Tai a ranar 21 ga watan Fabirairu 2023, bayan ya fice daga PDP ya komawa jam’iyyar APC, inda kuma bayan kwana biyu, aka shigar da karar Ogbonna Nwuke a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCRibasSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

Next Post

Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

2 seconds ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

38 minutes ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

3 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

7 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

8 hours ago
Next Post
Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

Buhari Da Iyalinsa Sun Isa Katsina Don Yin Zabe

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.