• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma

by CMG Hausa
3 years ago
Hijira

‘Yan gudun hijira mutane ne mafi fama da mawuyacin hali a duniya. Idan dai akwai dama, to, ba za su yi watsi da gidajensu, da barin iyalai, har su fita zuwa wata kasa ta daban ba, inda suke jure zaman rayuwa cike da wahalhalu. Sai dai yanzu har ana kara wulakanta su: Kasar da suke kaura cikinta ka iya tusa keyarsu zuwa wani wuri mai nisa, inda ba su taba tunani ko tsammanin zuwa ba.

A ranar 14 ga wata, kotun kare hakkin dan Adam ta nahiyar Turai ta hana tashin wani jirgin sama mai daukar nauyin jigilar ‘yan gudun hijira daga kasar Birtaniya zuwa Rwanda.

  • Xi Ya Yi Kira A Hada Gwiwa Don Yaki Da Rashawa

Kafin afkuwar lamarin, kasar Birtaniya da Rwanda sun kulla wata yarjejeniya, inda aka daddale cewa, Birtaniya zata biya kudi fam miliyan 120 ga Rwanda, don kasar Rwandan ta karbi ‘yan gudun hijira da suka yi satar ketarawa zuwa kasar Birtaniya. Ko da yake, ba a fara gudanar da yarjejeniyar ba tukuna, sakamakon kin amincewar da bangarorin kasa da kasa suka nuna, ciki har da hukumar ‘yan gudun hijira ta MDD suka nuna. Amma gwamnatin kasar Birtaniya tana ci gaba da neman aiwatar da yarjejeniyar.

Me ya sa ake kin amincewa da matakin da kasar Birtaniya ta dauka?
Saboda da farko dai, kasar Birtaniya, da Amurka, da sauran kasashen yammacin duniya, laifinsu ne yadda suka haddasa matsalar samun tarin ‘yan gudun hijira a duniya. Wadannan kasashe sun kaddamar da yake-yake a kasashen Iraki, da Afghanistan, da tsoma baki tare da tsananta yanayin rikici a Syria, da Libya, da Venezuela, da dai sauransu.

Hijira

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Irin matakan da suka dauka sune ainihin dalilan da suka haddasa karuwar ‘yan gudun hijira a duniya. Saboda haka ya kamata kasashen yamma su dauki nauyin kula da ‘yan gudun hijira, maimakon a tusa keyarsu zuwa wata kasar dake nahiyar Afirka.

Ban da wannan kuma, matakin kasar Birtaniya ya nuna wani yanayi na rashin adalci, inda matukar akwai kudi, to, ana iya yin kome. Su kasashe masu sukuni, sai su biya kudi, sa’an nan za su iya magance daukar nauyin kulawa da ‘yan gudun hijira.

Ganin haka zai sa su ta da rikici, da lalata yanayin zaman rayuwar jama’ar sauran kasashe, ba tare da wata damuwa ba. Idan an samu ‘yan gudun hijira, sai a tusa keyarsu zuwa kasashe masu tasowa, ba tare da tsoron samun wani tasiri daga lamarin ba.

Sa’an nan lamarin ya nuna halayyar kasashen yamma a fannin hakkin dan Adam. Da ma kasashen suna kallon kansu a matsayin “Masu kare hakkin dan Adam a duniya”, har ma su kan tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashe.

Sai dai ko da gaske ne suna kare hakkin dan Adam a duniya? Idan mun dauki kasashen Amurka da Birtaniya a matsayin misali. Kasar Amurka ta yi ta kaddamar da yake-yake a kasashe da dama, inda take kisan mutanen kasashen, da aiwatar da mulkin danniya a duniya. Yayin da a nata bangare, kasar Birtaniya tana kallon ‘yan gudun hijira a matsayin kayayyaki, tana neman mika su ga sauran kasashe ba tare da kulawa da yanayin da wadannan mutane suke ciki ba.

Ta wadannan batutuwa, za mu iya ganin cewa, kasashen yamma kullum suna neman sanya sauran kasashe kulawa da hakkin dan Adam, maimakon su da kansu su yi haka.

Batun nan ya shaida gaskiyar wata tsohuwar magana dake cewa: “A yi bincike kan halayyar wani mutum bisa aikace-aikacensa, maimakon kalmomin da ya fada”. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Next Post
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.