• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Masu garkuwa

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar hallaka wasu mutum biyu da ake zargin ‘yan garkuwa da mutane ne sa’ilin da suka yi yunkurin garkuwa da wani mutum mai suna Usman Abdulhamid.

 

A wata sanarwar manema labarai da kakakin hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar tare da raba wa ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi, ya shaida cewar a bisa kokarinsu da himmarsu na dakile ta’addanci ne suka samu wannan nasarar.

  • Atiku Abubakar Ya Doke Tinubu, Obi Da Kwankwaso A Bauchi

Ya ce, a ranar 3 ga watan Maris wasu ‘yan bindiga suka mamaye gidan Alhaji Abdulhamid Muhammad da ke kauyen Rafin Cora a karamar hukumar Ningi domin su yi garkuwa da dansa mai suna Usman Abdulhamid dan shekara 28 a duniya.

Masu garkuwa

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

A kan hakan, shi Usman ya jajirce tare da tirjijewa, lamarin da har sai da ta kai masu garkuwan sun bude masa ruwan harsasai a cikinsa a lokacin da ya yi kokarin guje musu.

 

Wakil ya kara da cewa, “Cikin hanzari daga samun rahoton faruwar lamarin, hadakar jami’an ‘yansanda da ‘yan Bijilante a karkashin jagorancin DPO din Ningi, inda suka nausa zuwa wajen da abun ya faru domin taka wa masu garkuwan burki. Amma isarsu ke da wuya ‘yan garkuwa suka marabcesu da harbe-harbe.”

 

A matsayin maida martani, ‘yansandan su ma sun bude wuta ga masu garkuwan inda aka yi bata-kashi a tsakani.

Masu garkuwa

Ya ce, “Bisa shan karfinsu da ‘yansanda suka yi, biyu daga cikin masu garkuwan sun mutu, an kuma kwato bindiga kirar AK47 guda daya a wajen da aka fafatan.”

 

Ya kara da cewa, an samu nasarar ceto wanda suka yi kokarin garkuwa da shi tare da kaisa zuwa asibitin gwamnatin tarayya da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa domin nema masa kulawar likitoci.

 

“Tunin kuma aka dukufa wajen bin sawun masu garkuwa da mutanen domin tabbatar da an kamo su don su fuskanci shari’a,” Wakil din ya kara da fadi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version