• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar hallaka wasu mutum biyu da ake zargin ‘yan garkuwa da mutane ne sa’ilin da suka yi yunkurin garkuwa da wani mutum mai suna Usman Abdulhamid.

 

A wata sanarwar manema labarai da kakakin hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar tare da raba wa ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi, ya shaida cewar a bisa kokarinsu da himmarsu na dakile ta’addanci ne suka samu wannan nasarar.

  • Atiku Abubakar Ya Doke Tinubu, Obi Da Kwankwaso A Bauchi

Ya ce, a ranar 3 ga watan Maris wasu ‘yan bindiga suka mamaye gidan Alhaji Abdulhamid Muhammad da ke kauyen Rafin Cora a karamar hukumar Ningi domin su yi garkuwa da dansa mai suna Usman Abdulhamid dan shekara 28 a duniya.

Masu garkuwa

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

A kan hakan, shi Usman ya jajirce tare da tirjijewa, lamarin da har sai da ta kai masu garkuwan sun bude masa ruwan harsasai a cikinsa a lokacin da ya yi kokarin guje musu.

 

Wakil ya kara da cewa, “Cikin hanzari daga samun rahoton faruwar lamarin, hadakar jami’an ‘yansanda da ‘yan Bijilante a karkashin jagorancin DPO din Ningi, inda suka nausa zuwa wajen da abun ya faru domin taka wa masu garkuwan burki. Amma isarsu ke da wuya ‘yan garkuwa suka marabcesu da harbe-harbe.”

 

A matsayin maida martani, ‘yansandan su ma sun bude wuta ga masu garkuwan inda aka yi bata-kashi a tsakani.

Masu garkuwa

Ya ce, “Bisa shan karfinsu da ‘yansanda suka yi, biyu daga cikin masu garkuwan sun mutu, an kuma kwato bindiga kirar AK47 guda daya a wajen da aka fafatan.”

 

Ya kara da cewa, an samu nasarar ceto wanda suka yi kokarin garkuwa da shi tare da kaisa zuwa asibitin gwamnatin tarayya da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa domin nema masa kulawar likitoci.

 

“Tunin kuma aka dukufa wajen bin sawun masu garkuwa da mutanen domin tabbatar da an kamo su don su fuskanci shari’a,” Wakil din ya kara da fadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cika Alkawari Tushe Ne Ga Aiwatar Da Mulki

Next Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

2 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

4 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

6 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

7 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

8 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

9 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

LABARAI MASU NASABA

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO

An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO

July 12, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.