• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnoni: Za Mu Gyara Duk Matsalolin Da Aka Samu A Zaben Shugaban Kasa – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Zaben Mazabar Dan Majalisar Tarayya Na Kabba/Bunu/Ijumu Ta Kogi Bai Kammalu Ba —INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa INEC za ta yi dukkan abin da za ta iya domin tabbatar da a lokacin zaɓen gwamnoni an kauce wa maimaita duk wasu cikas ɗin da aka fuskata lokacin zaɓen shugaban shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

 

Yakubu ya yi wannan jaddadawa ce a lokacin da ya ke taro da Kwamishinonin Zaɓe na Ƙasa, domin bibiya da nazarin yadda hukumar ta gudanar da zaɓen 25 ga Fabrairu, 2023.

  • INEC Za Ta Bai Wa Tinubu Takardar Shaidar Lashe Zabe Da Yamma

Ya ce maƙasudin taron na su shi ne a tattauna cikas ɗin da aka samu da kuma tabbatar da cewa ba a sake maimaita faruwar haka a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi ba, wanda za a gudanar a ranar 11 ga Maris, 2023.

 

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

“Babu shakka zaɓen da aka gudanar a satin da ya gabata ya samu cikas da ƙalubalen da ke buƙatar magancewa da kuma hana sake afkuwar su da gaggawa. An ɗauki lokaci tare da shan matuƙar walaha wajen tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓe. Amma dai an fuskanci cikas wajen aiwatarwa.

 

“Waɗansu ƙalubalen da aka ci karo da su, bagatatan su ka faru, ba a yi zato ko tunanin hakan zai iya faruwa ba. Musamman matsalolin aikawa da kayan zaɓe, na’urorin sadarwa da tsarin fasahar zamani, halayyar wasu jami’an zaɓe, ɗabi’un wasu ejan-ejan na jam’iyyu da masu goyon bayan jam’iyyun sun ƙara kawo wa tsarin tafiyar da shirin naƙasu ko cikas.”

 

Yayin da ya ke yaba wa irin jajircewar da ‘yan Nijeriya su ka yi da halin dattakon da wasu shugabannin siyasa su ka nuna, Yakubu ya ce abin da ya faru a lokacin zaɓe ya zama wani babban darasi ga INEC, ta yadda ta gaggauta gano matsalolin da su ka faru, domin kauce wa sake faruwar irin haka a zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki ta jihohi, wanda za a yi zaɓen gwamnoni a jihohi 28, kuma za a zaɓi ‘yan majalisar dokoki har 996.

 

Yakubu ya ce a zaɓen ranar tilas ma’aikatan INEC su zage damtse sosai a lokacin zaɓen ranar 11 ga Maris.

 

“Duk ma’aikacin da aka kama ya na wasa ko rashin ɗaukar aikin sa da muhimmanci, ko na dindindin ne ko na wucin-gadi a lokacin zaɓen shugaban ƙasa, to kada a kuskura a bar shi ya yi aikin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokoki.

 

“Tilas kuma ya kasance an kai kayan zaɓe kwanaki kafin ranar zaɓe a dukkan ƙananan hukumomi.

 

“Kwamishinonin Zaɓe da aka tura jihohi za a ɗora wa laifin rashin kai kayan zaɓe zuwa ƙananan hukimomi da wuri. Haka babu wani dalilin da za a ƙi kai janareto a cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.”

 

Yakubu ya ce za a tabbatar an yi amfani da na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS a ranar zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihohi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

Next Post

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

11 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
INEC
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
INEC

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.