• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Saudiyya Da Iran Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Dawo Da Huldar Jakadanci Tare Da Sake Bude Ofisoshin Jakadanci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda kasashen Sin da Saudiyya da Iran suka sanar a ranar Jumma’ar da ta gabata, kasashen biyu wato Saudiyya da Iran, sun cimma matsaya, wadda ta hada da yarjejeniyar dawo da huldar jakadanci da ma sake bude ofisoshin jakadanci da sake tura jakadu a tsakaninsu cikin watanni biyu.

Karamin ministan harkokin wajen kasar Saudiyya, kuma mamba a majalisar ministocin kasar, kana mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Musaad bin Mohammed Al-Aiban, shi ne ya jagoranci tawagar kasar ta Saudiyya, yayin da sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran, Admiral Ali Shamkhani ya jagoranci tawagar kasar Iran a lokacin tattaunawar da ta gudana a birnin Beijing, fadar mulki kasar Sin daga ranakun 6 zuwa 10 ga watan Maris, kamar yadda wata sanarwar bangarorin uku da suka hada da kasashen Sin, Saudiyya da Iran suka bayyana.

  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Sanarwar ta ce, kasashen Saudiyya da Iran duk sun mika godiyarsu ga kasashen Iraki da Oman, bisa daukar nauyin gudanar da shawarwari da dama tsakanin shekarar 2021 zuwa ta 2022, da kuma shugabanni da gwamnatin kasar Sin da suka dauki nauyin gudanar da shawarwarin, gami da goyon baya da kuma gudummawar da ta kai ga samun nasarar shawarwarin.

Yayin da yake taya bangarorin biyu murnar daukar wani mataki na tarihi, daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan bangarorin biyu wajen samun ci gaba mai inganci kamar yadda aka cimma cikin yarjejeniyar, ta yin aiki don samun kyakkyawar makoma tare da yin hakuri da nuna hikima.

Ita ma MDD ta yi maraba da wannan yarjejeniya da kasashen Saudiyya da Iran din suka cimma ta sake farfado da huldar diflomasiyya a wannan rana, kana ta yaba da rawar da kasar Sin ta taka a wannan lamari. Bugu da kari, kasashen Oman, da Türkiye, da Lebanon, da Iraki da sauran kasashe, sun fitar da sanarwa, inda suka yi maraba da sanarwar hadin gwiwa da bangarorin uku suka fitar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi tsokaci kan tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen Saudiyya da Iran a nan birnin Beijing, wanda ya samu kulawa sosai daga bangarori daban-daban.

Kakakin ya ce, tare da hadin gwiwar bangarorin da abin ya shafa, tattaunawar da aka yi tsakanin kasashen na Saudiyya da Iran a birnin Beijing, ta haifar da kyakkyawan sakamako. Kasashen Saudiyya da Iran sun fitar da taswira da kuma lokacin da za a bi, wajen kyautata hadin gwiwarsu, wanda ya samar da wani ginshiki mai kyau, na ciyar da hadin gwiwarsu gaba da kuma sake bude wani sabon babi a huldarsu.

Kakakin ya jaddada cewa, kasar Sin ba ta nuna son kai ko kadan a yankin Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa, kasar Sin na mutunta matsayin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya, kasancewar wannan yanki nasu ne, kuma tana adawa da gasar siyasa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin ba ta da wata niyya, kuma ba za ta nemi cike wani gurbi ba, ko kuma kafa kungiyoyi na musamman, yana mai cewa, kasar Sin a ko da yaushe tana ganin cewa, ya kamata a ko da yaushe, makomar yankin Gabas ta Tsakiya ta kasance a hannun kasashen yankin. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Siminti Na Dangote Ya Samu Gaggarumar Riba Da Bunkasa A 2022

Next Post

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

2 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

3 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

5 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

1 day ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

1 day ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

1 day ago
Next Post
Manzon Allah

Bita Da Karashen Darasi A Kan Kyawon Cika Alkawari Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.