• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasancewar Mutane Masu Akidu Da Al’adu Daban-Daban Na Bukatar Hakuri Da Mutunta Juna

by Sulaiman
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasancewar Mutane Masu Akidu Da Al’adu Daban-Daban Na Bukatar Hakuri Da Mutunta Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar da wani taro a jiya, albarkacin ranar adawa da kalaman kiyayya ta duniya, inda zaunannen wakilin Sin dake majalisar Zhang Jun ya yi kira ga kasashen duniya su mutunta tare da hakuri da juna, kana su rika tattaunawa cikin adalci don yaki da kalaman kiyayya.

Kasar Sin ta kasance daya daga cikin kasashen da suka gabatar da kudurin ayyana ranar ta yaki da kalaman kiyayya a shekarar 2021, inda aka fara gudanar da ita karon farko a bana.

  • Xi Ya Yi Kira A Hada Gwiwa Don Yaki Da Rashawa

Kamar yadda wakilin na Sin ya bayyana, yaki da kalaman kiyayya na bukatar kasashe su mutunta ’yanci da moriyar juna, da watsi da girman kai. Matukar da gaske ana son cimma zaman lafiya a duniya, to ya kamata gwamnati ta zama abar koyi ga jama’arta.

Bai dace gwamnati ta rika yada karairayi da zarge-zarge ba, domin jama’arta za su yi koyi da ita, lamarin da zai haifar da gadon kiyayya mara tushe tsakanin al’ummomi. Misali, an ga yadda tsohon shugaban Amurka Donald Trump, ya rika danganta annobar COVID-19 da kasar Sin, lamarin da ya sa aka rika nuna kyama ga mutanen Sin da Asiya a kasar da sauran kasashen yamma. Ko a lokacin babban zaben kasar, irin furucinsa ne ya haifar da harin da magoya bayansa suka kai ginin majalisa ta Capitol a kasar.

Hakuri shi ne tushen zaman lafiya. Kasancewar mutane daban-daban, masu addinai da akidu da launi da al’adu daban-daban, na bukatar hakuri da mutunta juna. Hadin kan kasa da kasa don moriyar juna, cikin adalci da mutunta juna, zai iya tabbatar da zaman lafiyar da ake muradi.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

Haka zalika shirye-shirye kamar irin na abota tsakanin matasan Sin da Afrika dake zaman dandalin musaya, zai yi gagarumin tasiri wajen kawar da rashin fahimtar dake haifar da kiyayya.

A ganina, nan gaba, matasan Sin da Afrika da za su zama manyan gobe, za su kasance tamkar ’yan uwa ba tare da la’akari da bamban-bambacen dake tsakaninsu ba.

Irin wannan shiri da makamantansa, za su kawar da kyama da kiyayya don tabbatar da zaman lafiya da mutunci da kuma jituwa tsakanin al’ummomi. Wannan, shiri ne da ya kamata sauran kasashe su yi koyi da shi yayin da ake kokarin kawar da kiyayya a duniya. (Fa’iza Muhammad Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lukaku Ya Kusa Komawa Inter Milan A Matsayin Aro

Next Post

Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

Related

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

51 minutes ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

2 hours ago
Firaministan Sin Ya Yi Kira Ga Membobin BRICS Da Su Zamo Ginshikan Bunkasa Sauyi Ga Tsarin Jagorancin Duniya
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Ga Membobin BRICS Da Su Zamo Ginshikan Bunkasa Sauyi Ga Tsarin Jagorancin Duniya

3 hours ago
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

24 hours ago
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

1 day ago
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

1 day ago
Next Post
Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

LABARAI MASU NASABA

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

July 7, 2025
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

July 7, 2025
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

July 7, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Ga Membobin BRICS Da Su Zamo Ginshikan Bunkasa Sauyi Ga Tsarin Jagorancin Duniya

Firaministan Sin Ya Yi Kira Ga Membobin BRICS Da Su Zamo Ginshikan Bunkasa Sauyi Ga Tsarin Jagorancin Duniya

July 7, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

July 7, 2025
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

July 7, 2025
China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS

China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS

July 7, 2025
Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China

Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.