Bai wuce mako guda kenan da ayyana kanal Agbu Kefas a matsayin zababben gwamnan jihar Taraba ba amma shi da ubangidansa na siyasa, Gwamna mai barin gado Darius Ishaku, sun fara yakin cacar baki kan bashin albashin ma’aikatan gwamnatin jihar.
Kefas, a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai bayan nasarar da ya samu a zaben, ya yi alkawarin biyan duk wasu basukan albashin ma’aikata da gwamnatin Gwamna Ishaku ta rike musu, inda ya yi alkawarin biyan bashin cikin kwanaki 100 bayan rantsar da shi a 29 ga watan Mayu, 2023.
Sai dai Gwamna Ishaku a lokacin da yake mayar da martani ga alkawarin da Kefas ya yi, ya ce ma’aikatan jihar basu bin gwamnatinsa wani bashi Ballantana ya fara maganar cika wannan alkawari.
A wata sanarwa da aka raba wa manema labarai dauke da sa hannun mai baiwa gwamna Ishaku shawara kan harkokin yada labarai, Bala Dan-Habu, gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa da ikirarin Kefas inda ya ce gwamnatinsa tana biyan ma’aikatanta albashinsu, babu wanda ke binta bashin sisi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp