• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Aikin Titin Kano Zuwa Kaduna Da Gadar Neja A Ranar 15 Ga Mayu – Gwamnati

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Za A Kammala Aikin Titin Kano Zuwa Kaduna Da Gadar Neja A Ranar 15 Ga Mayu – Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, a jiya ya ce, ‘yan kwangilar da ke gudanar da aikin hanyoyin Kano zuwa Zariya da na Zariya zuwa Kaduna tare da aikin Gadar Neja na 2 za su kammala tare da mikasu a ranar 15 ga watan Mayun 2023.

Ya shaida hakan ne ga ‘yan jarida bayan kammala zaman Majalisar zantawar ta kasa (FEC), tare da cewa, shi ma aikin babban hanyar Legas zuwa Ibadan mai nisan kilomita 116 tare da manyan gadojinsa zai kammala kuma za a mika wa gwammati shi zuwa ranar 30 ga watan Afrilu.

  • NAHCON Ta Bai Wa Jihohi Wa’adin Awa 48 Da Su Tura Kudaden Aikin Hajjin 2023

Sannan, ya ce, an amince da fitar da naira biliyan 1.39 domin farfado da kwangila da nufin kammala shi na Gadar Uto karo na biyu mai nisan kilomita 2.6 a Ikenje da ke jihar Delta daga naira biliyan 4.435 zuwa biliyan 5.835.

Ya ce, “Aikin Gadar Loko-Oweto tunin aka kammala shi. Shi ma Gadar Ikom an kammala. Sakatariyar Gwamnatin tarayya a jihohin Nasarawa, Bayelsa da Zamfara da na Awka an kammalasu su din ma, kazalika, rukunin gidajen Zuba, da gidaje 700 sun zama a kimtse ko yanzu za a iya kaddamar da su,” ya kara da cewa.

Shi kuma ministan noma da raya karkara, Muhammad Abubakar, ya ce, bukatar gina shalkwatar ma’aikatar noma da bunkasa yankunan karkara na gwamnatin tarayya ya samu amincewa.

Labarai Masu Nasaba

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

A cewarsa, ana son a karon farko za a kashe naira biliyan 6 domin fara gudanar da aikin sabuwar Shalkwatar.

Abubakar ya ce, an tsara cewa ginin Shalkwatar mai hawa 10 za a kirasa da suna gidan noma.

Dangane da hauhawar farashin shinkafa, ya ce ana yin abubuwa da yawa don tabbatar da samun shinkafar da tabbatar da wadatuwarsa a cikin kasa, don kara rage farashinsa da saukinsa “Tun da Nijeriya ce ta daya a nahiyar Afirka wajen noman shinkafa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Next Post

Yanzu-yanzu: Sojoji Sun Yi Watsi Da Kaloli 53, Sun Fitar Da Sabbi 28 A Abuja

Related

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa
Labarai

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

3 hours ago
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa
Labarai

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

6 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

7 hours ago
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

10 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Sojoji Sun Yi Watsi Da Kaloli 53, Sun Fitar Da Sabbi 28 A Abuja

Yanzu-yanzu: Sojoji Sun Yi Watsi Da Kaloli 53, Sun Fitar Da Sabbi 28 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.