• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Kasar Sin na kafa ‘tarkon bashi’ a Afirka, tana kafa ‘sabon salon mulkin mallaka’……” A cikin ’yan shekarun baya bayan nan, kafofin yada labarai na kasashen yamma sun sha yayata irin wadannan karairayi, a kokarin lalata huldar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka da ma hadin gwiwarsu.

Kaza lika a kwanakin baya, irin wadannan kafofi sun kara fitar da wani tsokacin, inda jaridar “The Times” ta Burtaniya, a wani rahotonta mai taken “Sinawa na ba ’yan tawayen Najeriya rashawa, don neman mallakar albarkatun ma’adinai”, ta zargi kasar Sin da “samar da kudin tallafi ga harkokin ta’addanci a Najeriya.”

  • Richard Sears: Harufan Sinanci Ba Kawai Na Kasar Sin Ba Ne, Al’ada Ce Mai Daraja Ga Duniya Baki Daya

Rahoton dai ya yi matukar jawo hankalin al’ummar Najeriya, har ma wasu da suke shan wahalar ta’addanci, da ma hare-haren ’yan tawaye sun fara nuna shakku ga hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. A game da hakan, Ambassada Isma’il Ahmed, mai sharhi kan harkokin diplomasiyya a Najeriya, a yayin tattaunawa da mu ya yi nuni da cewa, “ba wai wani abun mamaki ba ne don sun yi amfani da kafafen yada labaransu, ko jaridu wajen sukar China, ai sun sha yi.”

Ambassada Isma’il Ahmed ya ce, “A cikinsu guda hudu kamar Sudan, Aljeriya, Najeriya da Masar, dukkanninsu za ka ga suna da man fetur, kuma China na sayen fetur daga wajensu, don haka dole Turawa su ta da hankalinsu, kuma har gobe tagomashi ake samu ta fuskar cinikayya da tattalin arziki. Duk kamfanonin da suke Najeriya yanzu, suke ayyukan gine-ginen hanyoyin mota, da na layin dogon jiragen kasa, da tasoshin jiragen sama, dukkan kamfanoni ne na China, saboda sun fi sauki, sun fi dadin alaka, sun fi amana, sun fi gudanar da komai ba tare da an sa siyasa a ciki ba. Saboda haka zai yi wahala nan gaba a ce wai Turawa za su samu hanyoyin da ake tunanin za su yi amfani da su, domin fitar da kasar China daga hulda da kasashen Afrika.

Yawanci su kasashen Turawa suna amfani da damar su ce wajen daurewa masu mulkin kama-karya gindi, su yi ta mulkin mallaka a kasashen Afirka, amma ka kula abubuwa suna ja baya a yanzu, masu mulkin mallakar su kan kare, kuma su kansu su kan karkata su koma bangaren China.”

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

To kamar dai yadda Ambassada Isma’il Ahmed ya fada, kasashen Afirka a matsayinsu na kasashe masu mulkin kai, suna da kwarewa wajen yanke shawara, kan ko hadin gwiwarsu da wata kasa na da amfani ko illa, kuma suna da ’yancin zabar abokan hadin gwiwa, kuma in an yi nazari, a cikin ’yan shekarun baya, hadin gwiwar cin moriyar juna a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya samar da kyawawan sakamako na a zo a gani.

A karshe wannan rahoto na “The Times”, ya ce, “Najeriya kamar za ta ci gaba da zabar kasar Sin ta fannin zuba mata jari a maimakon kasashen yamma. Bayan ziyarar da mataimakiyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris ta kai Afirka a wannan wata, mataimakin shugaban Nijeriya Yemi Osinbajo, ya yaba da alfanun da aka samu bisa ga tallafin da kasar Sin ta samar, kuma shi ma zababben shugaban Najeriya mai jiran gado Bola Ahmed Tinubu, tuni ya zanta da jakadan kasar Sin.”

A hakika, kullum kasar Sin tana maraba da sassan kasa da kasa, da su aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, kuma sau tari ta sha bayyana cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasashen duniya, a maimakon fagen takarar manyan kasashe.

Karya dai fure take ba ta ’ya’ya, wadanda suke makircin lalata hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, muna ba su shawarar mai da hankalinsu a kan taimakawa kasashen Afirka, wajen tabbatar da ci gabansu a maimakon su rika yayata karairayi. Kasar Sin na maraba da karin kasashe su sa hannu a ayyukan raya Afirka, amma kuma tana adawa da niyya, da matakai na shafawa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka bakin fenti. Baya ga haka, muna kuma jan hankalin abokanmu na Nijeriya, da kada su fada cikin tarkon da kasashen yamma suka dana na dakile bunkasuwarsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri A Fadar Gwamnati A Abuja.

Next Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

5 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

7 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

7 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

11 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

12 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

13 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.