• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Sanya Sunan Pele Cikin Kamus A Brazil

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
An Sanya Sunan Pele Cikin Kamus A Brazil
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lakabin Pelé, da ake fada wa marigayi gwarzon dan kwallon duniya, bisa ka’ida ya shiga cikin kamus, inda yake nufin “zakakuri ko fintinkau ko abu na daban kamar yadda aka tabbatar”.

Kamusun harshen Portugal mai suna Michaelis, daya daga cikin mafi shahara a Brazil, ya sa sunan “Pelé” a matsayin sabuwar kalmar siffa a kundinsa na intanet kuma za’a ci gaba da amfani da kalmar.
Sanya sunan Pele a cikin kamus, ya zo ne bayan wani gangami da gidauniyar Pele ta kaddamar na neman a karrama tauraron dan kwallon, inda ya samu amincewa har mutane fiye da dubu 125,000 suka sa hannu.

Pele dai ya mutu a watan Disamban bara yana da shekara 82 a duniya kuma shi kadai ne dan kwallon da ya ci kofin duniya sau uku, kuma mutane da yawa na daukar sa a matsayin dan kwallon kafa mafi fice a tarihi.

A lokacin sana’arsa ta kwallon kafa tsawon shekara 20, Pele ya ci kwallaye masu yawa a tarihi har guda 1,281 lokacin da ya buga wa kungiyar Santos ta Brazil da kuma a kasar Brazil da kulob din Cosmos na New York.
Tun rasuwarsa, sanadin larurorin da ya yi fama da su na cutar dajin hanji, tsohuwar kungiyarsa Santos da tashar wasanni ta SporTB da gidauniyar Pelé suka yi ta matsa lamba don ganin an martaba sunan tauraron kwallon kafan na duniya, ta hanyar shigar da shi cikin kamus.

A ranar Laraba ne kuma, masu buga kamusun Michaelis suka sanar da cewa za’a shigar da kalmar cikin kundin kalmominsu na intanet a nan take kuma da zarar an zo wallafa kwafin takarda na kamus Michaelis nan gaba za a hada da kalmar pele.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

An sanya sunan kamar haka: “pe.lé adj. (siffa) Mutum wanda ya zarce saura, wanda nagartarsa, kima ko fifikonsa ba daya ne da komai ko da kowa ba, kamar dai Pelé, lakabin Edson Arantes do Nascimento, wanda ake dauka a matsayin dan wasa mafi gawurta a tsawon dukkan zamani kuma
zakakuri, mai fintinkau kuma na-daban.”

Gidauniyar Pelé, wadda kungiyar agaji ce da aka kafa don alkinta
tarihin gwarzon dan kwallon, ta ce karramawa ce da ta dace ga Pele kuma
Kalmar tuni ake amfani da ita wajen bayyana mutumin da ya yi fice kan
abin da yake yi, ta shiga shafukan kamus ta wallafa a sakon tuwita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Nijeriya Ake Sarrafa Taliyar Indomie, Ana iya Amfani Da Ita Ba Matsala – Shugabar NAFDAC

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

15 hours ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

1 day ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

2 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

4 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

4 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

4 days ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.