• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin $2m A Wajena, Ina Da Hujja –Matawalle

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin $2m A Wajena, Ina Da Hujja –Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya zargi shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Abdulrasheed Bawa, ya nemi ya ba shi toshiyar baki na Dala miliyan biyu.

Matawalle wanda ke cikin jerin wadanda EFCC ke zargi da badalalar biliyan 70 a halin yanzu, ya nuna cewa Bawa ya bukaci ya ba shi cin hancin amma da ya ki sai ya tasosa gaba.

  • An Kira Taron Karawa Juna Sani Game Da Daga Matsayin Alakar Sin Da Kasashen Afirka
  • An Fitar Da Rahoto Game Da Mummunan Tasirin Salon Matsin Lamba Na Diflomasiyyar Amurka

“Bincike gaskiya ne, ba a hana a yi bincike ba, amma kuma ya kamata binciken ya zamo na kowa da kowa, don bai kamata a ce komai sai dai a ambaci gwamna ba, ai ba gwamna ne kadai ke da asusun ajiya ba.”

“Kamar yadda shugaban EFCC ya ce ya tanadi takardu na gwamnoni, to muna so ya nuna wa duniya takardu na wadanda yake aiki tare da su, sannan shi kansa ya kamata ya rubuta wa kansa takarda don a bincike shi saboda akwai zarge-zarge masu dumbin yawa a kansa,” A cewar Matawalle.

A hirarsa da BBC Hausa da wakilinmu ya bibiya, Matawalle ya kalubalanci Bawa da ya sauka daga kan kujerarsa ya bayar da damar a bincike shi ya ga irin abubuwan da za a bankado.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Gwamnan na Zamfara, ya ce “Akwai shaidu da dama wadanda idan ya sauka za a fito da su a gwada wa duniya cewa shi ba mai gaskiya ba ne. Ya sauka ya gani duk wadanda ke da wata shaida a kansa za su kawo a cikin lokaci kalilan.”

Gwamna Matawalle, ya kara da cewa “Akwai abin da shi shugaban EFCC ya san ya yi tsakaninsa da ni, ya san abin da ya roka ban ba shi ba a kan haka ya sani gaba.”

Sai dai ita ma hukumar ta EFCC ta kalubalanci gwamnan jihar Zamfarar, Bello Matawalle kan cewa idan yana da hujja a kan cewar shugabanta, Abdulrasheed Bawa na da hannu a ayyukan rashawa to ya kai kara wajen ‘yan sanda.

Da aka tuntubi shugaban hukumar, Malam Abdulrasheed Bawa, ya ce ai babu wani dan adama da yake 100 bisa 100 a duniya.

Ya ce, “Amma dai gwargwadon hali wadannan maganganu da gwamna Matawalle yake yi, wane ya yi kaza, ai sai ya fadi.”

Shugaban na EFCC ya ce, ‘’Idan ya san akwai wani gwamna ko minista da ya yi wani abu ya zo ya kawo, idan kuma ya ga cewa ni na yi wani abu ai akwai ‘yan sanda da wuraren da zai iya rubuta kara sai ya kai idan ya so sai a bincike ni, in ya so sai a gano wanda ke da gaskiya.”

An dai shiga takun saka tsakanin gwamnan da EFCC ne bayan da hukumar ta ce ta aike da goron gayyata ga wasu gwamnoni da za su sauka a karshen watannan domin ta bincike su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BawaCin HanciEFCCHujjaMatawalle
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasan Dambe: Dogon Dan Ladi Ya Doke Autan Kudawa

Next Post

Abin Da Sin Ke Kawowa Duniya Shi Ne Dama Da Inshora

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

9 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

21 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

1 day ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

3 days ago
Next Post
Abin Da Sin Ke Kawowa Duniya Shi Ne Dama Da Inshora

Abin Da Sin Ke Kawowa Duniya Shi Ne Dama Da Inshora

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.