• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tafiya Da Gwani Mai Dadi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tafiya Da Gwani Mai Dadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasashen Afirka ke kara nuna amincewa da kasar Sin a fannonin hadin gwiwar wanzar da ci gabansu, karin kasashen nahiyar na dada zurfafa hadin gwiwa, da bunkasa ci gaban alakar dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Hakan ne ma ya sa a baya bayan nan shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, yayin da yake karbar takardar kama aiki daga sabon jakadan Sin a kasar sa Zhou Ding, ya jaddada burinsa na fadada hadin kai da bangaren kasar Sin a fannoni daban daban.

  • Xi Jinping Ya Nanata Muhimmancin Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ga duk mai bibbiyar yanayin alakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe, ya kwana da sanin yadda Sin din ta jima tana tallafawa Zimbabwe wajen samar da ababen more rayuwa, ta hanyar samar da kudaden gudanar da manyan ayyukan raya kasa, ciki har da katafaren ginin ofishin majalissar dokokin kasar, da fadada tashar samar da lantarki ta tururi mai zafi, da sake fasali, da kuma fadada babban filin jiragen sama na Robert Mugabe, da zango na uku na aikin samar da hidimar wayar salula ga al’ummar kasar, ayyukan da suka yi matukar taka rawar gani a fannin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Zimbabwe.

Bahaushe kan ce “Tafiya da gwani mai dadi”. A gani na hakan ne ma ya sanya kasashe masu tasowa ke dada fifita alakar su da Sin, idan ana batun alakar kasa da kasa, kasancewar kasar Sin na nacewa manufar kaucewa tsoma baki cikin harkokin wajen sauran kasashe, da nuna adawa da takunkuman da kasashen yamma ke kakabawa sauran kasashe, ciki har da irin wadanda aka kakabawa kasar ta Zimbabwe.

Baya ga haka, kasar Sin ta yi cudanya, tare da mara baya ga kasashen Afirka, a fannin samar da tallafin yaki da annobar COVID-19 wadda a ’yan shekarun da suka gabata ta addabi duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Hakan ne ma ya sa masharhanta da yawa ke hasashen kara kyautatuwa, da yaukaka, da dorewar alakar Sin da abokan tafiyarta wato kasashe masu tasowa, wadanda suka amince su yi tafiya kafada da kafada da Sin din bisa mutunta juna, da zurfafa musaya a fannonin hadin gwiwa daban daban, karkashin manufofi irin na “Shawarar ziri daya da hanya daya”, da manufar bunkasa ci gaban duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Rusashshiyar Kungiyar G-5

Next Post

Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Related

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam
Daga Birnin Sin

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

13 hours ago
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

14 hours ago
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

15 hours ago
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

16 hours ago
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

17 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

18 hours ago
Next Post
Isra’ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa ‘Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

Isra'ila Ta Kaddamar Da Manhajar Da Za Ta Samarwa 'Yan Nijeriya Miliyan Daya Ayyukan Yi

LABARAI MASU NASABA

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

July 30, 2025
Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

July 30, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.