• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Bai Ji Gari Ba…

by CMG Hausa
2 years ago
Photo taken from a Kyodo News helicopter on Feb. 13, 2021, shows tanks at the crippled Fukushima Daiichi nuclear power plant storing treated radioactive water from the plant. The Japanese government decided on April 13, 2021, to release the water into the sea despite the worries of local fishermen. (Kyodo)
==Kyodo

Photo taken from a Kyodo News helicopter on Feb. 13, 2021, shows tanks at the crippled Fukushima Daiichi nuclear power plant storing treated radioactive water from the plant. The Japanese government decided on April 13, 2021, to release the water into the sea despite the worries of local fishermen. (Kyodo) ==Kyodo

Yanzu haka hankalin duniya ya karkata kan matakin kasar Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku, duk da kashedin da masana da sassan kasa da kasa ke yi mata game da illar yin hakan ga duniya baki daya.

Tun lokacin da Japan ta bijiro da wannan aniya a shekarar 2021, bayan da wata girgizar kasar ranar 11 ga watan Maris din shekarar 2011 da ta lalata tashar nukiliyar Fukushima, tare da haddasa yoyon sinadarin nukiliya, aka rika nusar da Japan da ma wadanda suka bayar da shawarar aikata wannan danyen aiki.

  • Za A Bude Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka Karo Na 3

Idan ba a manta ba, shi ma taron kasashen nan 7 masu karfin tattalin arziki a duniya wato G7 da ya gudana a kasar ta Japan, bai goyi bayan shirin kasar na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku ba, saboda illarsa ga yanayin teku da tsaron abinci da ma lafiyar daukacin bil-Adama, amma bangaren Japan ya ci gaba da yin kememe da yin kunnen uwar shegu da neman kare kansa ta kowace hanya, wai don saboda arahar wannan tsari, wanda masu iya magana ke cewa, ba ta ado.

Idan har Japan ta damu da lafiya da tsaron al’ummarta da ma duniya baki daya, to ya kamata ta fahimci cewa, zubar da ruwan dagwallon nukuliya a cikin teku, batu ne da ya shafi duniya baki daya, saboda hadarin da ke tattara shi. Wannan ne ma ya sa a kwanakin baya wata tawagar masanan hukumar kula da makamashin nukuliya ta duniya IAEA ta ziyarci Japan, don gudanar da bincike bisa gaskiya da adalaci, da nufin fahimtar da mahukuntan kasar game da rashin fa’idar shirin ga rayuwar daukacin bil-Adama.

Don haka ya dace Japan ta bude ido da kunnuwanta ta kuma saurari abin da duniya ke fada game da illar da abin take son aiwatarwa. Idan kuma ta ki ji, to, ba za ta ki gani ba. Domin wanda bai ji gari ba, to kuwa zai ji Hoho. (Ibrahim Yaya)

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Dakatar Da Shugaban EFCC, Bawa Har Illa-masha Allah

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Dakatar Da Shugaban EFCC, Bawa Har Illa-masha Allah

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.