• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Kashe Wani Hardo Da Yaransa Hudu A Zariya

by Idris Umar
2 years ago
in Labarai
0
Mahara Sun Kashe Wani Hardo Da Yaransa Hudu A Zariya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Mahara sun kai hari gidan Ardon Birni da kewayen Zariya da ke kauyen Daurayi ta jihar kaduna, Alhaji Shuaibu Mohammed inda suka halaka shi tare da ’ya’yansa Hudu a daren ranar Asabar din da ta gabata.

Matar marigayin, Mallama Halima Shu’aibu ce ta sanar da manema labarai cewa, Maharan su biyar ne dauke da muggan makamai suka afka musu gida da misalin karfe 10:00 na dare sannan suka fada dakin Ardo inda suka kashe shi nan take.

  • Yadda Wani Jarimi Ya KuÉ“uta Daga ‘Yan Bindiga Bayan Sun Harbe Shi  A Kaduna

A cewar matar tasa daga nan nsai suka bi daki-daki na ’ya’yansa hudu, dukkansu magidanta, suka halaka su.

Matar ta bayyana sunayen ’ya’yansu da aka kashe a wannan harin da suka hada da Adamu Shuaibu, Musa Shuaibu, Abubakar Shuaibu da Haruna Ibrahim.

Halima ta kara da cewa bayan sun kashe su sai kuma suka kora shanunsu kimanin guda 100 a cikin daren.

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Shi ma da yake magana da manema labarai, daya daga cikin ’ya’yan Ardon da ya rage, Abdurrahman Shuaibu ya ce bayan sun gama da gidansu, maharan har ila yau sun kuma harbi mutane biyu a kan hanyarsu ta barin kauyen.

Da manema labarai suka tuntubi mai magana da yawun Rundunar ’Yansandan Jihar Kaduna, Mohammed Jalige, ya ce zai tuntubi babban jami’in ’yansanda na Zariya don jin cikakken bayanin yadda abin ya faru.

Sai dai har ya zuwa lokacin hada wannan rahoton bai kira don tabbatar da faruwar lamarin ba.

Ya zuwa yanzu jama’a nata jajanta wa kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wani Jarimi Ya KuÉ“uta Daga ‘Yan Bindiga Bayan Sun Harbe Shi  A Kaduna

Next Post

Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Ta Jihar Kano Ta Kafa Kwamitoci Don Sake Inganta Harkokinta

Related

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

57 minutes ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

2 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

5 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

6 hours ago
An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

7 hours ago
Next Post
Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Ta Jihar Kano Ta Kafa Kwamitoci Don Sake Inganta Harkokinta

Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Ta Jihar Kano Ta Kafa Kwamitoci Don Sake Inganta Harkokinta

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.