• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum 3 Da Ake Zargi Da Yin Garkuwa Da Wani Limami A Ondo

Na Yi Tafiya Ta Tsawon Sa'o'i 6 A Dajin - Babban Liman

by Muhammad
2 years ago
Ondo

Rundunar ‘yansandan jihar Ondo ta cafke masu garkuwa da malamin addinin musulunci, Alli Ibrahim Bodunde, wadanda aka yi garkuwa da shi a unguwar Uso da ke karamar hukumar Owo ta jihar a makonnin da suka gabata.

Wadanda ake zargin sun yi garkuwa da babban limamin unguwar Uso mai shekaru 67 a gonarsa da ke sansanin Asolo. An sake shi ne bayan da Jama’ar yankin suka biya kudin fansar naira miliyan 2.

Da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar ‘yan sanda da ke titin Igbatoro a Akure, babban birnin jihar, Kakakin ‘yan sandan Jihar, Funmilayo Odunlami-Omisanya, ya ce wadanda ake zargin su ne Muinah Mohammed mai shekaru 19 da Aisha Bello mai shekaru 20 da kuma Isah Bello mai shekaru 40.

Odunlami-Omisanya ya ce; “A ranar 18 ga watan Yuni, 2023, wata Misis Bodunde da misalin karfe 6 na yamma ta je ofishin ‘Yan sanda na Uso inda ta yi korafin cewa mijinta, Alli Ibrahim Bodunde ya je gona kuma ya kamata ya dawo da misalin karfe 2 na rana amma abin takaici har yanzu bai dawo ba.

“Lokacin da ’yan uwa ba su gan shi ba, sai suka tura mutum biyu zuwa gona domin nemansa.

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

“Lokacin da suka isa gona sai suka hadu da motarsa ​​da wayarsa amma ba su gan shi ba.

“Kuma nan take aka kai rahoton lamarin, ‘yan sanda suka shiga aikin, inda a karshe aka sako mutumin.

“Amma a dalilin binciken mun gano cewa mutumin da ake magana a kai shi ne babban limamin al’ummar Uso.

“Ta hanyar jami’an leken asirinmu, mun samu nasarar cafke wadanda ake zargin kuma a karshen binciken za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Labarai

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos
Labarai

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Next Post
Masarautar Zazzau Ta Dakatar Da Marafan Yamman Zazzau Kan Daukar Doka A Hannunsa

Masarautar Zazzau Ta Dakatar Da Marafan Yamman Zazzau Kan Daukar Doka A Hannunsa

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.