• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa Wajen Kare Mabanbantan Wayewar Kan Al’umma

by CMG Hausa
2 years ago
Sin

Rahotannin na cewa, an sake samun wani da ya kona Alkur’ani mai tsarki a kasar Sweden, lamarin da al’ummun kasashen Larabawa, da sauran musulmin duniya suka yi matukar Allah wadai da shi, yayin da kuma al’ummun kasa da kasa ke nuna damuwa da aikata hakan. 

Da take tsokaci kan hakan, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce har kullum kasar ta na yayata akidar martaba juna, da tafi tare da dukkanin sassa, da koyi da juna tsakanin mabanbantan wayewar kai. Kaza lika Sin na adawa da duk wani tsattsauran ra’ayi na kaiwa addinai hari, ko tunzura fito na fito tsakanin al’ummu, ko kyamar musulunci.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Yi La’akari Da Kimiyya Wajen Kawar Da Ruwan Dagwalon Nukiliyarta

Mao, wadda ta bayyana hakan yayin taron manema labarai na Talatar nan, ta ce wayewar kan musulunci ta bayar da gagarumar gudummawa ga ci gaban duniya, kuma ya zama wajibi a martaba akidun musulunci da musulmi. A daya hannun, bai kamata a fake da ‘yancin fadin albarkacin baki wajen rura wutar tashin hankali tsakanin mabanbantan wayewar kai ba.

A watan Maris din shekarar nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarar bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun kasa da kasa, inda ya yi kira da a aiwatar da manufofin daidaito, da koyi da juna, da tattaunawa, da tafiya tare tsakanin dukkanin wayewar kan al’ummun duniya.

Kasar Sin ta shirya tsaf, ta yi aiki da sauran sassan kasa da kasa, wajen yayata ruhin wannan shawara ta bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun duniya, da ingiza musaya tsakanin mabanbantan al’adu, da cimma matsaya ta aiwatar da matakai na hakika, da hada gwiwa wajen kare kimar mabanbantan wayewar kan al’ummun duniya. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
Kudure-Kuduren Gwamnatinmu Sun Dauki Hanyar Kai Nijeriya Matakin Nasara – Tinubu

Kudure-Kuduren Gwamnatinmu Sun Dauki Hanyar Kai Nijeriya Matakin Nasara – Tinubu

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.