• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da karar da Sanata Mohammed Danjuma Goje, ya shigar a gabanta na kalubalantar korara da kwamitin jami’yyar APC na mazabar Kashere da ke jihar Gombe ya yi masa.

Kwamitin ya dakatar da Goje ne daga baya kuma ya kore shi daga APC a watan Afrilu, 2023.

  • INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe
  • Masarautar Zazzau Ta Dakatar Da Marafan Yamman Zazzau Kan Daukar Doka A Hannunsa

Kwamitin ya kore shi ne, bisa zargin kin shiga ayyukan gangamin yakin neman zaben APC a dukkan matakai har da na yakin neman zaben shugaban kasa da kuma yi wa ‘yan takarar majalisar dikokin jihar da tarayya zagon kasa a lokacin yankin neman zaben.

Goje ya kuma ki yi wa shugabannin jami’yyar da’a da kuma kin yin biyayya ga mahukuntan da ke jagorantar jam’iyyar a jihar.

An kori Goje daga APC ne, bayan da kwamitin APC na mazabar Kashere ya mika rahotonsa na binciken zargin da ake yi wa Goje.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

A cikin rahoton kwamitin, ya gano cewa, zargin da ake yi wa Goje, ya tabbata, inda kwamitin ya bayar da shawarar a gaggauta dakatar da shi da kuma korarsa daga jam’iyyar.

Shugabancin APC na mazabar Kashere sun amince da rahoton kwamitin binciken, inda kuma babban kwamitin APC na jihar Gombe da sauran kwamitocin kananan hukumomi 11 na jihar, su ma suka amince da rahoton kwamitin da ya dakatar tare da korar Goje daga APC.

Bisa wannan dakatarwar ne da kuma korarsa, hakan ya sa Goje ya garzaya zuwa kotun don kalubalabatar matakin.

Sai dai, a hukuncin da alkalin babbar kotun da ke Abuja wadda mai shari’a alkali Obiora Egwatu ke jagoranta a zaman da ta yi a ranar Talata, ta yi fatali da karar da Goje ya shigar a gabanta na kalubalantar dakatar da shi da kuma korarsa daga APC.

Ko a ciki watan Mayu, kwamitin zartarwa na APC na kasa ya janye maganar korar Goje daga APC.

A cikin sanarwar da sakataren yada labarai na APC na kasa, Felix Morka ya fitar ya sanar da cewa, korar ta Goje an jingine ta a gefe har sai an yi nazari akan matakin da APC reshen jihar ya dauka.

Alkali Egwuatu ya tabbatar da cewa, korafin Goje na rashin yi masa adalci don ya kare kansa daga zarge-zargen da kwamitin ya yi masa, bai da wata hujja, domin kwamitin ya ba shi isashen lokaci don ya kare kansa.

Kotun ta ce Goje na sane da zarge-zargen da ake yi masa, musamman ganin cewa wata jarida ta wallafa zarge-zargen da ake yi masa, inda hakan ya ke da damar ya kare kansa da kuma ba shi damar lokaci da wurin da zai kare kansa.

A martanin da babban kwamitin APC na jihar Gombe ya yaba da hukuncin da kotun ta yanke.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGojeGombeHukunciKoraKotuMataki
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe

Next Post

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

4 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

7 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

7 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

9 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

10 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

10 hours ago
Next Post
Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.