• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan Habasha Abiy Ahmed, ya gana da daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Wang Yi jiya Jumma’a, inda bangarorin biyu suka yi alkawarin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Wang Yi ya kai ziyara kasar Habasha ne a kan hanyarsa ta hakartar taron masu ba da shawara kan harkokin tsaron kasa na kasashen BRICS karo na 13, da zai gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu.

  • Masani Habasha Ya Yi Karin Haske Kan Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

A yayin ganawarsa da Wang, Abiy Ahmed ya yi karin haske kan manyan nasarorin da kasar Sin ta cimma, yayin da take bin tafarkin gurguzu mai sigar musamman na kasar Sin, yana mai cewa, ya yaba da yadda kasar Sin take nacewa kan tafarkin ci gaba da ya dace da yanayin kasarta, gami da saurin bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewa da ta samu, wanda ya zama abin koyi ga ragowar kasashe masu tasowa.

A nasa bangaren kuwa, Wang Yi ya bayyana cewa, Habasha babbar kasa ce a nahiyar Afirka da ke da tasiri mai mahimmanci. Yana mai cewa a matsayinsu na abokan huldar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, Sin da Habasha suna da buri daya, kuma sun gudanar da hadin gwiwa mai inganci bisa tsare-tsare irin su “shawarar ziri daya da hanya daya” da dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ke jagorantar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Ban da haka, Wang Yi shi ma ya gana da mataimakin firaministan kasar Habasha kuma ministan harkokin wajen kasar Demeke Mekonnen.

Labarai Masu Nasaba

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yayin ganawar, Wang ya ce, kasar Sin tana goyon bayan kasar Habasha wajen kiyaye ikonta mulkin da cikakkun yankunanta, da goyon bayan kasar wajen cika alkawarin da ta dauka na tabbatar da hadin kai da zaman lafiyar kasar, tana kuma goyon bayanta wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin shiyya-shiyya da na kasa da kasa.

Ya kara da cewa, Sin na son yin aiki tare da Habasha wajen aiwatar da manufar zaman lafiya da ci gaba a yankin kahon Afirka, da tallafa wa jama’ar Afirka wajen warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da Afirka.

A nasa bangaren, Mekonnen ya bayyana cewa, kasar Habasha tana da dadadden tarihi wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kuma tana da niyyar karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin a matakan kasashen biyu, da shiyya-shiyya da kuma sassa daban-daban.

Ya ce, Habasha ta yaba da irin taimakon da kasar Sin take ba ta, wajen kiyaye tsaro da zaman lafiyarta, tana kuma fatan kasar Sin za ta kara taimaka mata wajen tabbatar da zaman lafiya, da aiwatar da gyare-gyare, da ma farfado da tattalin arzikinta yadda ya kamata.

Bugu da kari, shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto, ya gana da Mr. Wang Yi a birnin Nairobi na kasar Kenya a yau Asabar, inda bangaorin 2 suka bayyana niyyar raya huldar dake tsakanin kasashen 2 zuwa wani sabon mataki. (Ibrahim Yaya, Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Gero A Duniya Za Ta Kai Dala Biliyan 12 A 2025 -Masana

Next Post

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Related

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare
Daga Birnin Sin

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

3 hours ago
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243
Daga Birnin Sin

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

4 hours ago
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

4 hours ago
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

6 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

7 hours ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

1 day ago
Next Post
Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.