• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya ce da yiyuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta kirkiro wasu sabbin ma’aikatu da za su zama kari kan wadanda ake da su. 

Femi ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis a Abuja, inda ya ce bayan jerin ministoci 28 da Tinubu ya gabatar, zai kuma sake aikewa da sunayen mutum 13 nan gaba kadan.

  • Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes
  • Gwamman Zamfara Ya Karrrama Hajiyar Da Ta Tsinci Dala 80,000 A Saudiyya

Ya ce, ministocin da aka gabatar sai da suka tsallake tantancewar shugaban kasa da kansa.

Ya ce ba ya ga sunan mutum 28 da Tinubu ya gabatar a matsayin ministoci, zai kuma sake aikewa da kashi na biyu na ministocin da suka kunshi sunayen mutum 13.

“Kamar yadda kuka sani kwanaki 60 da rantsuwa, kamar yadda yake kunshe cikin kundin tsarin mulki. Ya cika ka’idar ya gindaya ta hanyar tura sunayen mutum 28 a yau.

Labarai Masu Nasaba

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

“Kamar yadda aka karanta cikin wasikarsa a gaban majalisar dattawa, akwai karin sunayen da za a gabatar, babu tabbacin su nawa ne amma wakila za su haura 12, za a tura sunayen ga majalisar dattawa nan da ‘yan kwanaki.”

Kamfanin Dillacin Labarai (NAN) ta ruwaito cewa Gbajabiamila ne ya gabatar da jerin sunayen ministocin da Tinubu ya zaba kuma shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta a majalisar.

Ministocin da aka zaba 28 su ne: Abubakar Momoh, Yusuf Maitama Tuggar, Ahmed Dangiwa, Hannatu Musawa, Chif Uche Nnaji, Dokta Betta Edu, Dokta Doris Aniche Uzoka, David Umahi da Nyesom Wike.

Sauran su ne Badaru Abubakar, Nasiru Ahmed El-Rufai, Ekperipe Ekpo, Nkeiruka Onyejocha, Olubunmi Tunji Ojo, Stella Okotette, Uju Kennedy Ohaneye, Mista Bello Muhammad Goronyo, Mista Dele Alake, da Mista Lateef Fagbemi.

Akwai kuma Mista Muhammad Idris, Mista Olawale Edun, Mista Waheed Adebayo Adelabu, Misis Iman Suleiman Ibrahim, Farfesa Ali Pate, Farfesa Joseph Utsev, Sanata Abubakar Kyari, Sanata John Enoh, da kuma Sanata Sani Abubakar Danladi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociMukamiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamza Abara Ya Zama Sabon Kocin Niger Tornadoes

Next Post

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Related

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

51 minutes ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

6 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

6 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

10 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

21 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

22 hours ago
Next Post
Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

Kutsen Yanar Gizo Da Take Kaiwa Sin Ya Shaida Damuwar Amurka A Fannin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.