• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Fct

A kalla daraktoci biyu da wasu jami’ai biyar na sashin kula da filaye na hukumar bunkasa babban birnin tarayya (FCDA) da sashin kula da harkokin cigaba (DDC) na fuskantar tuhume-tuhume a gaban ‘yansanda kan zarginsu da ake yi da tafka badakar fili. 

 

A cewar ‘yansandan, za a gurfanar da wadanda ake tuhuma a gaban kotu nan ba da jimawa ba.

  • FCTA Ta Rusa Kasuwar Dare Da Ke Asokoro, Abuja 

Wannan matakin na zuwa ne a dai-dai lokacin da sabon ministan babban birnin tarayya Mista Nyesom Wike ya sha alwashin dakile duk wata harkar filaye ta barauniyar hanya a kokarinsa na kwato asalin taswirar birnin tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Tuhume-tuhumen da ‘yansanda ke musu sun hada da aikata babban laifi, amfani da takardar bogi, karya da kuma sojan gona.

 

Wannan lamarin ya sanya ‘yansanda kaddamar da bincike kan takaddamar waye hakikanin mamallakin fili a tsakanin kamfanin ‘Cona Engineering and Technical Services Nigeria Limited’ da kuma wani Yusuf Daniel Ogwu kan filin da ke lamba 1308 Cadastral Zone A09 a gundumar Guzape, Abuja.

 

Kamfanin ta tura ma’aikata domin su fara aikin gini a filin kafin shi Yusuf Daniel Ogwu ya ankare tare da gabatar da shaidar R of O da ke ikirarin shi ne hakikanin mamallakin filin.

 

Sai dai kuma takardun da ke akwai sun nuna cewa takardar shaidar mallaka COG an mallaka wurin ne ga Jamila Saleh Hassan a ranar 6 ga watan Yunin 2007 (file No: 20400), da ta kasance mai cin gajiya kuma mamallakiyar filin mai lamba 1308 Cadastral Zone A09 gundumar Guzape, Abuja.

 

Jamila Saleh Hassan, ta kyautar da wurin ga wani Sunday Benjamin Egele a wani watan Yunin 2014.

 

Kazalika, shi ma Sunday Benjamin Egele ya kyautar da wurin ga kamfanin Cona Engineering and Technical Services Limited, a watan Disamban 2018.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
Next Post
Nijar Ta Sake Bude Sararin Samaniyarta Bayan Juyin Mulki

Nijar Ta Sake Bude Sararin Samaniyarta Bayan Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.